Home Labarai NLC ta zargi ‘Yan sanda da dukan shugabanta

NLC ta zargi ‘Yan sanda da dukan shugabanta

Kungiyar kwadago ta kasa ta zargi rundunar ‘yansanda ta kasa da lakadawa shugabanta na kasa Joe Ajaero duka, bayan sun yi awon gaba dashi a tsakar ranar jiya a jihar Imo.

Shugaban yada labarai da hulda da jama’a na kungiyar, Benson Upah shine ya baiyana haka ta cikin wata sanarwa da ya fitar a daren laraba, lokacin da yake tabbatar das akin shugaban nasu, bayan ya wuni a hannun jami’an yansanda.

Jami’an yansanda sunce sun tsare shugaban kungiyar kwadagon ta kasa ne domin bashi kariya bayan ya fuskanci cin zarafi.

Sai dai jim kadan da sakin shugaban kungiyar kwadagon ta kasa kwamared Joe Ajaero ya tabbatar da cewar an lakada masa duka sannan aka yi awon gaba dashi zuwa wani wuri da bai sani, wanda a nan ne aka gallaza masa.A wani labarin kuma Hukumar Kula Da Yanayi Tayi Hasashen Samun Hazo Da Kura A ‘Yan Kwanaki Masu Zuwa

Gwamnatin tarayya ta ce yanzu haka shirye-shirye sunyi nisa domin sauya akalar motoci har milyan 10 masu amfani da man fetir zuwa amfani da Gas nan da watanni 36 masu zuwa.

Karaminin ministan Mai, Ekperikpe Ekpo ne ya baiyana haka a yayin baje kolin mai da iskar gas na shekarar bana wanda ake gudanarwa a birnin Abu Dhabi na hadaddiyar daular larabawa.

A wata sanarwa da kakakinsa Louis Ibah ya fitar, ya baiyaan cewar a yanzu haka anyi kawance da kanfanoni masu zaman kansu domin kawo kayayyakin da za’a yi amfani dasu wajen sauya akalar motocin nan da watanni 9 masu zuwa.

Ya ce matakin wani yunkuri ne na inganta yin amfani da Gas a tsakanin motocin kasar a maimakon Man fetir da suka dogara dashi.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp