Home Labarai shugaban hukumar NAHCON ya bukaci a rage kudin Hajjin bana.

shugaban hukumar NAHCON ya bukaci a rage kudin Hajjin bana.

Mukaddashin shugaban hukumar NAHCON, Malam Jalal Ahmad Arabi, ya bukaci hukumomin jin dadin Alhazai na jihohin Nijeriya da su yi dukkan mai yiwuwa wajen ganin sun rage kudin hajjin shekarar 2024.

ya bayyana hakan ne ranar Alhamis yayin da yake karbar bakuncin sakatarori da shuwagabannin, da kuma shuwagabannin sojojin Nijeriya a shalkwatar hukumar dake birnin tarayya Abuja.

haka kuma ya bukaci su dasu sanya kudin da suka karba zuwa yanzu a asusun hukumar ta NAHCON, domin adadin kudin su zasu bayyana mataki na gaba da za’a dauka.

“babu lokaci, ya kamata ku sanya kudin da kuka karba a Asusun NAHCON, domin yin shirye 0 shiryen farko kafin aikin Hajjin, gami da ziyara domin kulla alaka da ayyukan da za’a gudanar a yayin aikin hajjin.

“ta yadda mutanen mu zasu gansu da kokarin mu da nasarorin da zamu samu sakamakon shirin da mukayi don aikin hajjin shekarar 2024 ya zo cikin sauki,” a cewar sa.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp