Home Labarai Tinubu zai fara biyan sabon tsarin mafi karancin albashi.

Tinubu zai fara biyan sabon tsarin mafi karancin albashi.

Gwamnatin Najeriya ta ce sabon tsarin mafi karancin albashi zai fara aiki daga ranar ɗaya ga watan Afrilun 2024.

Ministan yaɗa labarai da wayar da kan jama’a na kasar, Idris Mohammed, wanda ya bayyana hakan a wata hira da ya yi da manema labarai a Abuja, ya ce tsarin mafi ƙarancin albashi na naira 30,000 na yanzu zai daina aiki ne a karshen watan Maris na shekarar 2024.

Mohammed ya bayyana haka ne a ranar Alhamis, yayin nazarin kasafin kudi na shekarar 2024-2026 da shugaba Tinubu ya gabatar inda ya ce za a kashe naira tiriliyan 24.66 kan albashi a shekarar 2024 da 2025 da kuma 2026.

Bayan cire tallafin man fetur da Tinubu ya yi a ranar 29 ga watan Mayun 2023, gwamnatin tarayya ta amince ta bai wa kowane ma’aikacinta tallafin naira 35,000 domin rage raɗaɗin cire tallafin.

Sai dai kungiyar ƙwadago ta dage kan cewa tallafin naira 35,000 na wucin-gadi bai wadatar ba, inda ta kara da cewa ya kamata a sake duba mafi karancin albashi a shekarar 2024.

Tawagar Gwamnatin Tarayya da Majalisar Tattaunawar Ma’aikata ta Kasa a ranar 18 ga Oktoba, 2019, sun amince da aiwatar da mafi karancin albashi na naira 30,00 bayan shafe watanni ana tattaunawa.

Sai dai a ranar Alhamis kungiyar kwadago ta tabbatar da cewa ta fara tattaunawa da gwamnatin tarayya, inda ta kara da cewa bisa tsarin dokar kwadagon kasar ya kamata a sake duba mafi karancin albashi duk bayan shekaru biyar.

Shugaban Kungiyar Kwadago ta Najeriya, Joe Ajaero, ya ce kwanan nan, “Sake duba mafi ƙarancin albashi na kasa lamari ne na doka da ake sa ran zai faru a 2024.”

A nasa ɓangaren, ministan yaɗa labarai da wayar da kan jama’a, Mohammed, ya shaida  cewa, ƙarin albashin na da nufin maye gurbin matakin wucin-gadi da gwamnati ta sanya don magance wahalhalun da ke tattare da cire tallafin man fetur.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp