Home Labarai Tinubu zai fara biyan sabon tsarin mafi karancin albashi.

Tinubu zai fara biyan sabon tsarin mafi karancin albashi.

Gwamnatin Najeriya ta ce sabon tsarin mafi karancin albashi zai fara aiki daga ranar ɗaya ga watan Afrilun 2024.

Ministan yaɗa labarai da wayar da kan jama’a na kasar, Idris Mohammed, wanda ya bayyana hakan a wata hira da ya yi da manema labarai a Abuja, ya ce tsarin mafi ƙarancin albashi na naira 30,000 na yanzu zai daina aiki ne a karshen watan Maris na shekarar 2024.

Mohammed ya bayyana haka ne a ranar Alhamis, yayin nazarin kasafin kudi na shekarar 2024-2026 da shugaba Tinubu ya gabatar inda ya ce za a kashe naira tiriliyan 24.66 kan albashi a shekarar 2024 da 2025 da kuma 2026.

Bayan cire tallafin man fetur da Tinubu ya yi a ranar 29 ga watan Mayun 2023, gwamnatin tarayya ta amince ta bai wa kowane ma’aikacinta tallafin naira 35,000 domin rage raɗaɗin cire tallafin.

Sai dai kungiyar ƙwadago ta dage kan cewa tallafin naira 35,000 na wucin-gadi bai wadatar ba, inda ta kara da cewa ya kamata a sake duba mafi karancin albashi a shekarar 2024.

Tawagar Gwamnatin Tarayya da Majalisar Tattaunawar Ma’aikata ta Kasa a ranar 18 ga Oktoba, 2019, sun amince da aiwatar da mafi karancin albashi na naira 30,00 bayan shafe watanni ana tattaunawa.

Sai dai a ranar Alhamis kungiyar kwadago ta tabbatar da cewa ta fara tattaunawa da gwamnatin tarayya, inda ta kara da cewa bisa tsarin dokar kwadagon kasar ya kamata a sake duba mafi karancin albashi duk bayan shekaru biyar.

Shugaban Kungiyar Kwadago ta Najeriya, Joe Ajaero, ya ce kwanan nan, “Sake duba mafi ƙarancin albashi na kasa lamari ne na doka da ake sa ran zai faru a 2024.”

A nasa ɓangaren, ministan yaɗa labarai da wayar da kan jama’a, Mohammed, ya shaida  cewa, ƙarin albashin na da nufin maye gurbin matakin wucin-gadi da gwamnati ta sanya don magance wahalhalun da ke tattare da cire tallafin man fetur.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp