Home Labarai Gwamnatin Jihar Kaduna ta magantu kan harin sojoji kan masu Maulidi

Gwamnatin Jihar Kaduna ta magantu kan harin sojoji kan masu Maulidi

Gwamnatin jihar kaduna ta dora alhakin harin daya hallaka mutane sama da 30 a jihar Kaduna kan dakarun sojojin saman Nijeriya.

ta cikin wata sanarwa da kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida na jihar Samuel Aruwan ya fita ta bayyana cewa gwamantin jihar ta sami wani bayanin tsaro a daren ranar lahadi dake cewa wani harin sama kan fararen hula yayi sanadiyyar mutuwar mutane masu tarin yawa a jihar dake arewa maso yammacin kasar.

a yayin wani taron majalisar tsaro bisa jagorancin mataimakiyar gwamnan Jihar Dr. Hadiza Sabuwa Balarabe, wanda ya sami halartar shuwagannin tsaro da na gargajiya, rundunar sojojin Nijeriya ta yi bayani kan lamarin wanda ya haifar da harin.

Jagoran dake lura da shiyya ta daya ta dakarun sojin Manjo VU Okoro ya yi bayyana cewa dakarun sojojin na zagayen ganin sun kawar da ‘yan ta’adda amma cikin kuskure harin ya hau kan Al’ummar dake cikin garin.

mataimakiyar gwamnan a yayin rufe taron ta miki ta’aziiyar gwamnatin jihar ga Al’ummar jihar kaduna da ‘yan uwa da iyalan wadanda harin ya rutsa da su, tare da neman gafara ga wadanda lamarin ya auku a kan su.

taron dai ya samu halartar kwamshinan ‘yan sandan jihar My Garba, daraktan hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) Abdul Eneche, shugaban kungiyar JNI na jihar Kaduna Farfesa Shafi’u Abdullahi, wanda ya jagoranci shuwagabannin addinai, haka kuma akwai dagacin Rigasa Alhaji Aminu Idris wanda a yankin sa harin ya faru.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp