Home Labarai Gwamnatin Jihar Kaduna ta magantu kan harin sojoji kan masu Maulidi

Gwamnatin Jihar Kaduna ta magantu kan harin sojoji kan masu Maulidi

Gwamnatin jihar kaduna ta dora alhakin harin daya hallaka mutane sama da 30 a jihar Kaduna kan dakarun sojojin saman Nijeriya.

ta cikin wata sanarwa da kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida na jihar Samuel Aruwan ya fita ta bayyana cewa gwamantin jihar ta sami wani bayanin tsaro a daren ranar lahadi dake cewa wani harin sama kan fararen hula yayi sanadiyyar mutuwar mutane masu tarin yawa a jihar dake arewa maso yammacin kasar.

a yayin wani taron majalisar tsaro bisa jagorancin mataimakiyar gwamnan Jihar Dr. Hadiza Sabuwa Balarabe, wanda ya sami halartar shuwagannin tsaro da na gargajiya, rundunar sojojin Nijeriya ta yi bayani kan lamarin wanda ya haifar da harin.

Jagoran dake lura da shiyya ta daya ta dakarun sojin Manjo VU Okoro ya yi bayyana cewa dakarun sojojin na zagayen ganin sun kawar da ‘yan ta’adda amma cikin kuskure harin ya hau kan Al’ummar dake cikin garin.

mataimakiyar gwamnan a yayin rufe taron ta miki ta’aziiyar gwamnatin jihar ga Al’ummar jihar kaduna da ‘yan uwa da iyalan wadanda harin ya rutsa da su, tare da neman gafara ga wadanda lamarin ya auku a kan su.

taron dai ya samu halartar kwamshinan ‘yan sandan jihar My Garba, daraktan hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) Abdul Eneche, shugaban kungiyar JNI na jihar Kaduna Farfesa Shafi’u Abdullahi, wanda ya jagoranci shuwagabannin addinai, haka kuma akwai dagacin Rigasa Alhaji Aminu Idris wanda a yankin sa harin ya faru.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp