Home Labarai Gwamnatin Jihar Kaduna ta magantu kan harin sojoji kan masu Maulidi

Gwamnatin Jihar Kaduna ta magantu kan harin sojoji kan masu Maulidi

Gwamnatin jihar kaduna ta dora alhakin harin daya hallaka mutane sama da 30 a jihar Kaduna kan dakarun sojojin saman Nijeriya.

ta cikin wata sanarwa da kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida na jihar Samuel Aruwan ya fita ta bayyana cewa gwamantin jihar ta sami wani bayanin tsaro a daren ranar lahadi dake cewa wani harin sama kan fararen hula yayi sanadiyyar mutuwar mutane masu tarin yawa a jihar dake arewa maso yammacin kasar.

a yayin wani taron majalisar tsaro bisa jagorancin mataimakiyar gwamnan Jihar Dr. Hadiza Sabuwa Balarabe, wanda ya sami halartar shuwagannin tsaro da na gargajiya, rundunar sojojin Nijeriya ta yi bayani kan lamarin wanda ya haifar da harin.

Jagoran dake lura da shiyya ta daya ta dakarun sojin Manjo VU Okoro ya yi bayyana cewa dakarun sojojin na zagayen ganin sun kawar da ‘yan ta’adda amma cikin kuskure harin ya hau kan Al’ummar dake cikin garin.

mataimakiyar gwamnan a yayin rufe taron ta miki ta’aziiyar gwamnatin jihar ga Al’ummar jihar kaduna da ‘yan uwa da iyalan wadanda harin ya rutsa da su, tare da neman gafara ga wadanda lamarin ya auku a kan su.

taron dai ya samu halartar kwamshinan ‘yan sandan jihar My Garba, daraktan hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) Abdul Eneche, shugaban kungiyar JNI na jihar Kaduna Farfesa Shafi’u Abdullahi, wanda ya jagoranci shuwagabannin addinai, haka kuma akwai dagacin Rigasa Alhaji Aminu Idris wanda a yankin sa harin ya faru.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp