Home Labarai Rundunar sojin Nijeriya ta yi nadamar kai harin kan masu Maulidi

Rundunar sojin Nijeriya ta yi nadamar kai harin kan masu Maulidi

Miscalculated Bombardment of Kaduna Civilians Regretted – Nigerian Military

Rundunar Sojojin Nijeriya ta bayyana harin da jirgin ta ya kai kan masu gudanar da taron mauludi a kauyen Ligarma dake jihar kaduna matsayin kuskure.

daraktan yada labaran rundunar, Manjo Janar Edward Buba, ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa da ya fitar ranar talata, inda sanarwa tace dakarun na sintirin kawar da ‘yan ta’addan sun hangi giftawar ‘yan ta’addan a kauyen.

yace na’urar sintirin ta hango zirga-zirga wasu mutane da suka yi kama da ‘yan ta’adda wannan ce ta sanya aka kai harin.

“an kai harin ne domin gani an dakile yunkunrin ‘yan ta’adda na gudanar da ayyukan su na ta’addanci kan fararen hula.”

yace dakarun sojojin na yin iyaka kokarin su wajen rarrabe al’ummar gari da ‘yan ta’adda. “sojojin na kallon rasa ran dukkan farar hula matsayin abin ki a duk lokacin da irin wannan ta auku.

Buba yace dakarun sojojin na daukar matakan da suka dace wajen kaucewa rasa rayukan fararen hula, daga cikin su kuwa harba bayar da umarnin da Al’umma dake rayuwa a yankunan dake fuskantar matsalar ‘yan ta’addan na su sanar da sojojin.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp