Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cewa yana cikin alhini tare da al’ummar jihar Ondo, bisa rasuwar gwamnansu, Rotimi Akeredolu.
A cikin wata wasiƙa da ya fitar, Tinubu ya ce “Ba za mu sake ganin mutum kamarsa ba”.
Ya ce gwamnatinsa za ta karrama Gwamna Rotimi don ganin ba a mance da hidimar da ya yi wa al’umma ba.
Read Also:
Tinubu ya ce tuni ya yi wayar tarho da uwargidan marigayin Betty da kuma mai riƙon muƙamin gwamnan jihar Lucky Aiyedatiwa inda ya miƙa ta’aziyyarsa gare su kan wannan rashi.
Ya bayyana Gwamna Akeredolu ba kawai a matsayin aboki ba, ɗan’uwansa ne kuma shaƙiƙi. Ya bayyana mutuwar a matsayin babban rashi ga jam’iyyarsu ta APC mai mulki da kuma iyalai ma’abota rajin ci gaba.
PRNigeria Hausa