Abba Gida-gida ya kaddamar da ayyukan sabbin gadoji

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya aza harsashin ginin gada mai hawa uku da zata lashe Naira biliyan 27  a mahadar Dan’agundi, da kuma Tal’udu duk a cikin birnin Kano.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da babban daraktan yada labaran gwamnan Kano, Sanusi Bature Dawakin tofa ya fitar kuma aka raba manema labarai a jihar.

A yayin a aza harsashin ginin, gwamnan ya ce an fara gudanar da manyan ayyukan ne domin rage cunkoson ababen hawa, da saukaka zirga-zirga, da kawata birnin, da hana gurbatar muhalli, da samar da ababen more rayuwa ga al’umma.

Haka Kuma gwamnan ya nanata alkawuran gwamnatinsa na samar da ababen more rayuwa a jihar tare da kudurin samar da karin ribar dimokuradiyya musamman ga wadanda aka zalunta.

Ya ce  matsayin jihar na babban birni ta cancanci a samar da gagarumin sauyi na ababen more rayuwa domin biyan bukatun mazauna birnin sama da miliyan goma da inganta zamantakewa da tattalin arzikin mazauna birnin.

PRNigeria hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 26 minutes 10 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 11 hours 7 minutes 35 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com