• Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Search
  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Sign in
Welcome! Log into your account
Forgot your password? Get help
Password recovery
Recover your password
A password will be e-mailed to you.
PRNIGERIA PRNigeria Hausa
PRNIGERIA PRNIGERIA
  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Home Labarai Atiku Abubakar ya kalubalanci Tinubu kan tsadar rayuwa a Nijeriya
  • Labarai

Atiku Abubakar ya kalubalanci Tinubu kan tsadar rayuwa a Nijeriya

By
Ozumi Abdul
-
December 31, 2023
Arewa Award

Tsohon mataimakin shugaban Kasar Najeriya Atiku Abubakar ya ce dole ne gwamnati mai ci ta ɓullo da hanyar magance wahalhalun da ƴan Najeriya ke ciki a wannan lokaci.

Atiku ya bayyana haka ne a sakonsa na barka da sabuwar shekara ga ƴan Kasar. inda ya ce dole gwamnati ta nuna wa ƴan ƙasa alkibla ko kuma inda manufofinta suka dosa ba wai barinsu a cikin duhu ba.

“Da gwamnati ta yi dabara wajen tsara manufofinta da ba mu shiga irin wannan kangi da muke ciki ba. Iyalai da kuma masana’antu da yawa na cikin wane hali a yanzu,” in ji Atiku.

Read Also:

  • Natasha ta halarci zaman majalisar Dattawa karon farko bayan dakatar da ita
  • Muna so majalisa ta gaggauta amincewa da sabbin dokokinmu – INEC
  • DSS ta gurfanar da Sowore a kotu kan zargin ‘aibata’ Tinubu a shafin X

Ya ce ya zama tilas a tashi domin fuskantar batun hauhawar farashin kayayyaki, taɓarɓarewar tattalin arziki da kuma rashin tsaro a sabuwar shekara da nufin magance su.

Tsohon mataimakin shugaban ƙasar ya ce shekara ta 2023 na cike da kalubale masu tarin yawa, sai dai ya kamata a ɗauki darasi domin fuskantar gaba.

“Idan muna son fita daga wannan kunci da muke ciki, dole ne mu yi tunani mai kyau da kuma samar da tsare-tsare na ƙasa waɗanda za su sa talakawan Najeriya su zama ginshikin ci gaban mu,” in ji Atiku.

Wazirin na Adamawa ya taya dukkan ƴan Najeriya murnar sabuwar shekara tare da yin kira ga kowa da ya tashi haikan don ganin iyalai da sana’o’in sun kasance cikin yanayi mai kyau.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Previous articleƳan sanda sun kuɓutar da malamin jami’ar jihar Nasarawa
Next articleGwamnatin Nijeriya zata karbe lasisin masu hakar ma’adinai
Ozumi Abdul

RELATED ARTICLESMORE FROM AUTHOR

Natasha ta halarci zaman majalisar Dattawa karon farko bayan dakatar da ita

Muna so majalisa ta gaggauta amincewa da sabbin dokokinmu – INEC

Gwamnatin Najeriya ta ce za ta ci gaba da ciyo bashi duk da samun ƙarin kuɗaɗen shiga-

Gwamnan Kano ya tarɓi masu zanga-zangar ƙin kalaman Lawan Triumph

Gwamnatin Kano ta yi gargaɗi kan zazzaɓi mai tsanani da ke sa mutum zubar da jini

Taswirar Katsina

Ƴan bindiga sun sako mutane 40 bayan sulhu da mahukuntan Katsina

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta tabbatar da mutuwar jami’anta a Jihar Benue

Nasarar da Daliban Kano suka Samu a NECO kokarin Ganduje ne – Sanusi Kiru

Wata kotun Majistiri a Kano ta bawa Jami’an KAROTA umarni

Sojojin Najeriya sun cafke kwamandan IPOB

Ƴanbindiga sun hallaka mutum 22 a Jamhuriyyar Nijar

NDLEA ta kama Ba’indiye da wasu mutane da ƙwaya ta naira biliyan uku a Legas

Recent Posts

  • Natasha ta halarci zaman majalisar Dattawa karon farko bayan dakatar da ita
  • Muna so majalisa ta gaggauta amincewa da sabbin dokokinmu – INEC
  • DSS ta gurfanar da Sowore a kotu kan zargin ‘aibata’ Tinubu a shafin X
  • Gwamnatin Najeriya ta ce za ta ci gaba da ciyo bashi duk da samun ƙarin kuɗaɗen shiga-
  • Gwamnan Kano ya tarɓi masu zanga-zangar ƙin kalaman Lawan Triumph

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1573 days 3 hours 35 minutes 54 seconds,



Baptist School Students, Kaduna
1555 days 5 hours 17 minutes 19 seconds

Report By: prnigeria.com/hausa

Book on Sales: Boko Haram Media War: An Encounter with the Spymaster

boko haram

Click Here:To Order Now!

  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
© 2020 PRNigeria. All Rights Reserved.
Latest News
Natasha ta halarci zaman majalisar Dattawa karon farko bayan dakatar da itaMuna so majalisa ta gaggauta amincewa da sabbin dokokinmu - INECDSS ta gurfanar da Sowore a kotu kan zargin 'aibata' Tinubu a shafin XGwamnatin Najeriya ta ce za ta ci gaba da ciyo bashi duk da samun ƙarin kuɗaɗen shiga-Gwamnan Kano ya tarɓi masu zanga-zangar ƙin kalaman Lawan TriumphGwamnatin Kano ta yi gargaɗi kan zazzaɓi mai tsanani da ke sa mutum zubar da jiniƳan bindiga sun sako mutane 40 bayan sulhu da mahukuntan KatsinaRundunar ƴan sandan Najeriya ta tabbatar da mutuwar jami'anta a Jihar BenueNasarar da Daliban Kano suka Samu a NECO kokarin Ganduje ne - Sanusi KiruWata kotun Majistiri a Kano ta bawa Jami'an KAROTA umarniSojojin Najeriya sun cafke kwamandan IPOBƳanbindiga sun hallaka mutum 22 a Jamhuriyyar NijarSojojin Nijeriya sun hallaka mayakan boko haram 5 a jihohin Borno da TarabaNDLEA ta kama Ba'indiye da wasu mutane da ƙwaya ta naira biliyan uku a LegasLikitoci a Najeriya sun janye yajin aikin gargaɗi
X whatsapp