• Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Search
  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Sign in
Welcome! Log into your account
Forgot your password? Get help
Password recovery
Recover your password
A password will be e-mailed to you.
PRNIGERIA PRNigeria Hausa
PRNIGERIA PRNIGERIA
  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Home Labarai Atiku Abubakar ya kalubalanci Tinubu kan tsadar rayuwa a Nijeriya
  • Labarai

Atiku Abubakar ya kalubalanci Tinubu kan tsadar rayuwa a Nijeriya

By
Ozumi Abdul
-
December 31, 2023
Arewa Award

Tsohon mataimakin shugaban Kasar Najeriya Atiku Abubakar ya ce dole ne gwamnati mai ci ta ɓullo da hanyar magance wahalhalun da ƴan Najeriya ke ciki a wannan lokaci.

Atiku ya bayyana haka ne a sakonsa na barka da sabuwar shekara ga ƴan Kasar. inda ya ce dole gwamnati ta nuna wa ƴan ƙasa alkibla ko kuma inda manufofinta suka dosa ba wai barinsu a cikin duhu ba.

“Da gwamnati ta yi dabara wajen tsara manufofinta da ba mu shiga irin wannan kangi da muke ciki ba. Iyalai da kuma masana’antu da yawa na cikin wane hali a yanzu,” in ji Atiku.

Read Also:

  • NDLEA ta kama wani matashi da yayi safarar kwayoyin Tramadol dubu 7 daga Legas zuwa Kano
  • Bama goyan bayan ayyukan ta’addanci a Najeriya – Miyetti Allah
  • Sojoji sun hallaka ’yan fashi 7 a Katsina

Ya ce ya zama tilas a tashi domin fuskantar batun hauhawar farashin kayayyaki, taɓarɓarewar tattalin arziki da kuma rashin tsaro a sabuwar shekara da nufin magance su.

Tsohon mataimakin shugaban ƙasar ya ce shekara ta 2023 na cike da kalubale masu tarin yawa, sai dai ya kamata a ɗauki darasi domin fuskantar gaba.

“Idan muna son fita daga wannan kunci da muke ciki, dole ne mu yi tunani mai kyau da kuma samar da tsare-tsare na ƙasa waɗanda za su sa talakawan Najeriya su zama ginshikin ci gaban mu,” in ji Atiku.

Wazirin na Adamawa ya taya dukkan ƴan Najeriya murnar sabuwar shekara tare da yin kira ga kowa da ya tashi haikan don ganin iyalai da sana’o’in sun kasance cikin yanayi mai kyau.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Previous articleƳan sanda sun kuɓutar da malamin jami’ar jihar Nasarawa
Next articleGwamnatin Nijeriya zata karbe lasisin masu hakar ma’adinai
Ozumi Abdul

RELATED ARTICLESMORE FROM AUTHOR

Bama goyan bayan ayyukan ta’addanci a Najeriya – Miyetti Allah

Sojoji sun hallaka ’yan fashi 7 a Katsina

Shalkwatar tsaron Nijeriya ta yi karin bayani kan batun kare kai

Gwamnonin PDP na taro a Zamfara

Ya kamata kowane ɗan Najeriya ya koyi dabarar kare kai – Musa

Hukumar KAROTA ta kaddamar da kotun tafi da gidanka a jihar Kano

kotu ta dakatar da asusun banki huɗu na Mele Kyari

Ana neman mutane 40 a cikin Kogi bayan kifewar kwale-kwale a Sokoto

A biya mu haƙƙoƙinmu, ba mu son bashin gwamnati – ASUU

Amurka za ta sayar wa Nijeriya makamai da kuɗinsu ya kai dala miliyan 346

PDP za ta ƙaddamar da kwamitocin zartaswa na shiyoyi

EFCC ta ba da belin tsohon gwamnan Sokoto Tambuwal da ta tsare

Recent Posts

  • NDLEA ta kama wani matashi da yayi safarar kwayoyin Tramadol dubu 7 daga Legas zuwa Kano
  • Bama goyan bayan ayyukan ta’addanci a Najeriya – Miyetti Allah
  • Sojoji sun hallaka ’yan fashi 7 a Katsina
  • Shalkwatar tsaron Nijeriya ta yi karin bayani kan batun kare kai
  • Gwamnonin PDP na taro a Zamfara

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1530 days 6 hours 16 minutes 40 seconds,



Baptist School Students, Kaduna
1512 days 7 hours 58 minutes 5 seconds

Report By: prnigeria.com/hausa

Book on Sales: Boko Haram Media War: An Encounter with the Spymaster

boko haram

Click Here:To Order Now!

  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
© 2020 PRNigeria. All Rights Reserved.
Latest News
NDLEA ta kama wani matashi da yayi safarar kwayoyin Tramadol dubu 7 daga Legas zuwa KanoBama goyan bayan ayyukan ta'addanci a Najeriya - Miyetti AllahSojoji sun hallaka ’yan fashi 7 a KatsinaShalkwatar tsaron Nijeriya ta yi karin bayani kan batun kare kaiGwamnonin PDP na taro a ZamfaraYa kamata kowane ɗan Najeriya ya koyi dabarar kare kai - MusaHukumar KAROTA ta kaddamar da kotun tafi da gidanka a jihar Kanokotu ta dakatar da asusun banki huɗu na Mele KyariAna neman mutane 40 a cikin Kogi bayan kifewar kwale-kwale a SokotoA biya mu haƙƙoƙinmu, ba mu son bashin gwamnati - ASUUAmurka za ta sayar wa Nijeriya makamai da kuɗinsu ya kai dala miliyan 346PDP za ta ƙaddamar da kwamitocin zartaswa na shiyoyiEFCC ta ba da belin tsohon gwamnan Sokoto Tambuwal da ta tsareMajalisar Dokokin Kano ta Dakatar da Ciyaman din RanoƘananan dillalan mai sun zargi shugabanninsu da yiwa Matatar Dangote zagon ƙasa
X whatsapp