Home Labarai Tinubu Ya gana da Hafsoshin tsaron Kasar kan matsalar Tsaro

Tinubu Ya gana da Hafsoshin tsaron Kasar kan matsalar Tsaro

Shugaban Nijeriya Asiwajo Bola Tinubu ya gana da hafsoshin tsaron kasar da kuma wasu manyan hukumomin tsaro a fadarsa da ke birnin tarayya Abuja, a ranar Talata.

Hafsoshin tsaron da suka halarci ganawar sun haɗa da babban hafsan tsaro, Janar Christopher Musa, shugaban rundunar sojin ƙasa, Laftanar-Janar Taoreed Lagbaja, shugaban sojin sama, Air Marshal Hassan Abubakar, da kuma shugaban sojojin ruwa, Vice Admiral Emmanuel Ogalla.

haka kuma mai taimakawa shugaban ƙasa kan harkokin tsaro, Malam Nuhu Ribadu na cikin waɗanda suka halarci taron.

Sun tattauna kan batun karuwar aikata ta’addanci, garkuwa da mutane da kuma kashe-kashe a faɗin kasar da nufin magance su.

Nijeriya dai na guda cikin kasashen yammacin Afirka dake fama da matsalar rashin tsaro, kama daga masu garkuwa da mutane domin karbar kudin fansa dake cin karensu babu babbaka a yankin Arewa maso yamma da wasu jihohi a tsakiyar kasar.

sai kuma mayakan boko haram da na ISWAP dake tayar da kayar baya a yakin arewa maso Gabas, sai Kudu maso kudu da wasu yankuna a kudancin kasar dake fama da mayakan IPOB masu rajin kafa kasar Biyafara.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp