Gwamnatin tarayya ta kara ranar Alhamis matsayin ranar hutun sallah

Gwamnatin tarayyar Nijeriya ta ayyana ranar Alhamis 11 ga watan Afrilu, 2024 matsayin Kari cikin ranakun hutu a kasar, a wani bangare na bukukuwan karamar sallah ta shekarar 1445 bayan hijra.

Wannan na kunshe ne ta cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun babban sakatariyar ma’aikatar cikin gida Dr. Aishetu Gogo Ndayako.

Sanarwar ta ambaci ministan ma’aikatar Dr. Olubunmi Tunji-Ojo, na taya daukacin Al’ummar Musulmin kasar murnar kamala ibadar azumin watan Ramadan cikin kwanciyar hankali, inda kuma ya bayyana kudirin shugaban kasar Bola Ahmad Tinubu na samawa ‘yan kasar kyakkyawan yanayi.

Idan zamu iya tunawa jaridar PRNigeria ta ambaci ministan ya ayyana ranar talata 9 da kuma 10 ga watan Afrilun, 2024 matsayin ranakun hutun karamar a kasar.

 PRNigeria hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1189 days 15 hours 17 minutes 50 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1171 days 16 hours 59 minutes 15 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com