Home Labarai Kotu ta tabbatar da dakatar da Ganduje daga APC

Kotu ta tabbatar da dakatar da Ganduje daga APC

Wata babbar kotu a jihar Kano ta tabbatar da dakatarwar da aka yi wa shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje.

Idan dai za’a iya tunawa kwanaki biyu da suka gabata ne shugabancin APC na mazabar Ganduje a Karamar Hukumar Dawakin Tofa, mahaifar Ganduje, ya dakatar da shi bisa zargin cin-hanci da rashawa da gwamnatin Kano ke yi masa.

Ta cikin umarnin kotun, ƙarƙashin Mai Shari’a Usman Na’abba, ta hana Ganduje, wanda shine tsohon gwamnan Kano, nuna kan sa a matsayin shugaban jam’iyyar APC.

Na’abba ya kuma hana Ganduje yin wani taro ko daukar mataki a matsayin shugaban jam’iyyar har sai an kammala zaman sauraron karar.

Ya kuma hana shugabancin jam’iyyar na jiha shiga cikin maganar da take gaban kotu.

Dr. Ibrahim Sa’ad, a madadin biyu daga cikin shugabannin APC na mazabar Ganduje, mataimakin sakatare, Laminu Sani da mai baiwa jam’iyyar shawara kan harkokin Shari’a, Haladu Gwanjo ne ya shigar da karar.

Haka kuma kotun ta umarci waɗanda ake kara su hudu da suka haɗa da jam’iyar APC a matakin kasa da jiha da kuma shi Ganduje din da su tsaya a matsayin su daga 15 ga Afrilu zuwa 30 ga watan Afrilu lokacin da za a saurari karar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp