Home DUNIYA An dakatar da kafafen yaɗa labaran BBC da VOA a Burkina Faso

An dakatar da kafafen yaɗa labaran BBC da VOA a Burkina Faso

Hukumar da ke sa ido kan kafafen yaɗa labarai a Burkina Faso ta ƙaƙaba dakatarwar mako biyu kan kafar yaɗa labarai na BBC Afrique da Muryar Amurka (VOA) saboda yaɗa rahoton da ƙungiyar kare haƙƙin bil adama ta Human Rights Watch ta fitar da ke zargin sojojin ƙasar da cin zarafin farar hula.

Kazalila, hukumar ta dakatar da shafukan intanet na kafofin yaɗa labaran da ƙungiyar Human Rights a cikin ƙasar.

Kamfanin dillancin labarai na ƙasar ya ruwaito cewa “An umarci BBC da VOA ta hannun wakilansu a Burkina Faso da su gaggauta daina watsa shirye-shirye a dukkanin kafofinsu,”

Hukumar kula da harkokin sadarwa ta sake gargaɗin kafafen yaɗa labarai a ƙasar da su kaucewa yaɗa labarin inda ta yi barazanar ƙaƙaba wa waɗanda suka bijire takunkumi.

A ranar Alhamis ne ƙungiyar kare haƙƙin bil adama ta Human Rights Watch ta zargi sojojin Burkina Faso da kashe farar hula aƙalla 223 a arewacin ƙasar ranar 25 ga watan Fabarairu.

A Disamban 2023 ne Burkina Faso ta dakatar da jaridar French daily Le Monde kan zargin nuna son kai a rahotannin da suke yaɗawa.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp