Home DUNIYA An dakatar da kafafen yaɗa labaran BBC da VOA a Burkina Faso

An dakatar da kafafen yaɗa labaran BBC da VOA a Burkina Faso

Hukumar da ke sa ido kan kafafen yaɗa labarai a Burkina Faso ta ƙaƙaba dakatarwar mako biyu kan kafar yaɗa labarai na BBC Afrique da Muryar Amurka (VOA) saboda yaɗa rahoton da ƙungiyar kare haƙƙin bil adama ta Human Rights Watch ta fitar da ke zargin sojojin ƙasar da cin zarafin farar hula.

Kazalila, hukumar ta dakatar da shafukan intanet na kafofin yaɗa labaran da ƙungiyar Human Rights a cikin ƙasar.

Kamfanin dillancin labarai na ƙasar ya ruwaito cewa “An umarci BBC da VOA ta hannun wakilansu a Burkina Faso da su gaggauta daina watsa shirye-shirye a dukkanin kafofinsu,”

Hukumar kula da harkokin sadarwa ta sake gargaɗin kafafen yaɗa labarai a ƙasar da su kaucewa yaɗa labarin inda ta yi barazanar ƙaƙaba wa waɗanda suka bijire takunkumi.

A ranar Alhamis ne ƙungiyar kare haƙƙin bil adama ta Human Rights Watch ta zargi sojojin Burkina Faso da kashe farar hula aƙalla 223 a arewacin ƙasar ranar 25 ga watan Fabarairu.

A Disamban 2023 ne Burkina Faso ta dakatar da jaridar French daily Le Monde kan zargin nuna son kai a rahotannin da suke yaɗawa.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp