Home DUNIYA Amurka na shirin janye sojojinta daga Chadi

Amurka na shirin janye sojojinta daga Chadi

Amurka za ta janye wasu daga cikin dakarunta daga Chadi na wani ɗan lokaci, kwanaki bayan da ta amince ta janye duka dakarunta daga Nijar mai maƙwabtaka.

Sakataren yaɗa labarai na ma’aikatar tsaron Amurka Pentagon, Manjo Janar Pat Ryder ya ce Amurka za ta sakewa wasu daga cikin sojojin wuri daga Chadi amma bai ce suwa ne waɗanda matakin zai shafa ba ko kuma inda za a kai su.

“Wannan mataki ne na wucen gadi a yunƙurin sake nazari kan haɗin gwiwar tsaro da za a ci gaba da yinta bayan zaɓen shugaban ƙasar Chadi na ranar 6 ga watan Mayu.” kamar yadda ya bayyana.

Sanarwar ta zo ne bayan da shugaban hafsan sojin saman Chadi, a farkon watan nan, ya umarci Amurka ta dakatar da ayyukanta a sansanin sojin sama da ke N’Djamena, babban birnin Chadi, in ji kamfanin dillancin labarai na Reuters.

Gen Ryder ya kuma ce an soma tattaunawa da sojojin da ke mulki a Nijar da majalisar tabbatar da tsaron ƙasa CNSP ranar Laraba domin tabbatar da janye sojojin Amurka daga ƙasar cikin lumana.

Amurka ta dogara kan Nijar a matsayin babbar sansaninta ta bibiyar ayyukan ƴan ta’adda a yankin Sahel.

Sai dai sojojin Nijar da ke mulkin ƙasar tun Yuli, sun kawo ƙarshen yarjejeniyar tsaro da ƙasar tare da korar sojojin Faransa, wani yunƙuri na yanke alaƙa da ƙasashen yamma.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp