Home DUNIYA Fiye da mutum 40 sun mutu bayan fashewar madatsar ruwa a Kenya

Fiye da mutum 40 sun mutu bayan fashewar madatsar ruwa a Kenya

Mutane da dama sun rasa rayukansu bayan fashewar wata madatsar ruwa a yankin Mai Mahiu da ke Kenya, kamar yadda ƙungiyar agaji ta Kenya Red Cross ta shaida wa BBC.

Gwamna a yankin, Susan Kihika ma ta tabbatar da mutuwar mutanen ga kamfanin dillancin labarai na AFP.

Ruwa ya ɓalle inda ya tafi da gidaje da motoci da dama a ƙauyen Kamuchiri sakamakon mamakon ruwan sama da ake yi a yankuna da dama na ƙasar.

Tawagar agaji na lalube cikin taɓo domin zaƙulo masu sauran numfashi, in ji kafafen yaɗa labaran ƙasar inda kuma suka yi gargaɗin adadin mutanen da suka mutu na iya ƙaruwa.

Lamarin ya datse babban titin da ya tashi daga Nairobi zuwa Mai Mahu bayan da manya-manyan duwatsu da taɓo suka rufe hanyar.

Tun farko, ƙungiyar agaji ta Kenya Red Cross ta ce ta kai mutane da dama zuwa asibiti a Mai Mahiu saboda ambaliya.

Adadin mutanen da suka mutu a yanzu sakamakon mamakon ruwan sama da ambaliya a ƙasar tun watan da ya gabata sun zarce 100.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp