Home DUNIYA Fiye da mutum 40 sun mutu bayan fashewar madatsar ruwa a Kenya

Fiye da mutum 40 sun mutu bayan fashewar madatsar ruwa a Kenya

Mutane da dama sun rasa rayukansu bayan fashewar wata madatsar ruwa a yankin Mai Mahiu da ke Kenya, kamar yadda ƙungiyar agaji ta Kenya Red Cross ta shaida wa BBC.

Gwamna a yankin, Susan Kihika ma ta tabbatar da mutuwar mutanen ga kamfanin dillancin labarai na AFP.

Ruwa ya ɓalle inda ya tafi da gidaje da motoci da dama a ƙauyen Kamuchiri sakamakon mamakon ruwan sama da ake yi a yankuna da dama na ƙasar.

Tawagar agaji na lalube cikin taɓo domin zaƙulo masu sauran numfashi, in ji kafafen yaɗa labaran ƙasar inda kuma suka yi gargaɗin adadin mutanen da suka mutu na iya ƙaruwa.

Lamarin ya datse babban titin da ya tashi daga Nairobi zuwa Mai Mahu bayan da manya-manyan duwatsu da taɓo suka rufe hanyar.

Tun farko, ƙungiyar agaji ta Kenya Red Cross ta ce ta kai mutane da dama zuwa asibiti a Mai Mahiu saboda ambaliya.

Adadin mutanen da suka mutu a yanzu sakamakon mamakon ruwan sama da ambaliya a ƙasar tun watan da ya gabata sun zarce 100.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp