Home Labarai Ƙarin mayaƙan Boko Haram shida sun miƙa wuya ga dakarun MNJTF

Ƙarin mayaƙan Boko Haram shida sun miƙa wuya ga dakarun MNJTF

Rundunar dakarun ƙasashen da ke yaƙi da ƙungiyar Boko Haram ta MNJTF ta ce ƙarin ƴan ta’adda shida sun sake miƙa wuya tare da ajiye makamansu.

Jami’in yaɗa labarai na rundunar, leftena kanar, Abubakar Abdullahi ne ya tabbatar da hakan cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Litinin.

A cewar sanarwar, wani ɗan Boko Haram mai shekara 19 ya miƙa wuya ga sojojin runduna ta 403 da ke Monguno.

Binciken farko, a cewar sanarwar ta nuna cewa matashin na da alaƙa ta kusan shekara uku da ɓangaren Buduma na Boko Haram.

Ƙarin mayaƙa biyu – ɗan shekara 37 da 21 sun miƙa kansu a Blangua da ke Kamaru ga dakarun runduna ta ɗaya da ke yankin Darak a kudancin tafkin Chadi. Binciken da aka yi a kansu ya nuna ƴan asalin Chadi ne da ke zama a yankunan Kami-Wari da Kourea.

Sai kuma wani ɗan shekara 38 da mai ɗakinsa da ƴaƴansu biyu – ɗan shekara 13 da jaririya sun kai kansu ga sojojin runduna ta uku a yankin Baga da ke Najeriya.

Haka nan, sanarwar ta ce wani ɗan shekara 25 shi ma ya miƙa kansa ga sojojin runduna ta uku a Kekeno da ke ƙarmar hukumar Kukawa a jihar Borno inda ya bayyana cewa mayaƙan Boko Haram sun yi garkuwa da shi a kan titin Monguno zuwa Maiduguri a shekarar 2020.

Ya bayyana cewa a lokacin da aka kama shi, an tilasta masa yin aiki a matsayin mai gadi a ɗaya daga cikin sansanonin ƙungiyar da ke tafkin chadi.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp