Home Labarai Ƙarin mayaƙan Boko Haram shida sun miƙa wuya ga dakarun MNJTF

Ƙarin mayaƙan Boko Haram shida sun miƙa wuya ga dakarun MNJTF

Rundunar dakarun ƙasashen da ke yaƙi da ƙungiyar Boko Haram ta MNJTF ta ce ƙarin ƴan ta’adda shida sun sake miƙa wuya tare da ajiye makamansu.

Jami’in yaɗa labarai na rundunar, leftena kanar, Abubakar Abdullahi ne ya tabbatar da hakan cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Litinin.

A cewar sanarwar, wani ɗan Boko Haram mai shekara 19 ya miƙa wuya ga sojojin runduna ta 403 da ke Monguno.

Binciken farko, a cewar sanarwar ta nuna cewa matashin na da alaƙa ta kusan shekara uku da ɓangaren Buduma na Boko Haram.

Ƙarin mayaƙa biyu – ɗan shekara 37 da 21 sun miƙa kansu a Blangua da ke Kamaru ga dakarun runduna ta ɗaya da ke yankin Darak a kudancin tafkin Chadi. Binciken da aka yi a kansu ya nuna ƴan asalin Chadi ne da ke zama a yankunan Kami-Wari da Kourea.

Sai kuma wani ɗan shekara 38 da mai ɗakinsa da ƴaƴansu biyu – ɗan shekara 13 da jaririya sun kai kansu ga sojojin runduna ta uku a yankin Baga da ke Najeriya.

Haka nan, sanarwar ta ce wani ɗan shekara 25 shi ma ya miƙa kansa ga sojojin runduna ta uku a Kekeno da ke ƙarmar hukumar Kukawa a jihar Borno inda ya bayyana cewa mayaƙan Boko Haram sun yi garkuwa da shi a kan titin Monguno zuwa Maiduguri a shekarar 2020.

Ya bayyana cewa a lokacin da aka kama shi, an tilasta masa yin aiki a matsayin mai gadi a ɗaya daga cikin sansanonin ƙungiyar da ke tafkin chadi.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp