Home Labarai Kwamitin da aka kafa don bincikar gwamnatin Ganduje ya fara aiki

Kwamitin da aka kafa don bincikar gwamnatin Ganduje ya fara aiki

Kwamitin bincike da gwamnatin Kano ta kafa domin binciken batun zargin wadaƙa da dukiyar al’umma ya fara zamansa na farko.

Kwamitin zai yi bincike ne tsakanin 2015 da 2023, wato zamanin mulkin, Dr Abdullahi Umar Ganduje, inda ake fatan kwamitin zai karɓi ƙorafe-ƙorafe daga jama’a da kuma ‘yan ƙungiyoyi a kan yadda tsohon gwamnan ya yi tasarrufi da kadarorin gwamnati.

A kwanakin baya ne gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf ya kafa kwamatocin bincike biyu da za su binciki zargin al’mundahana da rikicin siyasa da ɓatan mutane a jihar, al’amarin da ya haifar da zazzafar muhawara.

Kwamitin binciken ƙarkashin jagorancin mai shari’a Faruk Lawan Adamu, ya ce al’umma suna da damar zuwa kwamitin, su gabatar da duk wani ƙorafi ko rashin gamsuwa da yadda aka tafiyar da gwamnatin jihar Kano daga 2015 zuwa 2023.

Barista Bashir Sale mamba ne a kwamitin binciken kuma ya yi wa BBC ƙarin bayani game da farko da kwamitin ya yi.

Ya ce “kadarorin gwamnati – makarantu da filaye da gidaje, maƙabartu da burtali, ya ya aka yi da su? An sayar? bisa ƙa’ida aka sayar? Idan ba bisa ƙa’ida aka sayar ba, wa ya siya, idan kuma ka siya, wa ka siyarwa?

Ya kuma ce za su bi ƙa’ida da yin adalci a binciken da za su yi.

Nan gaba ne kuma za a fara sauraron bahasi daga ɓangarori daban-daban ciki har da duk wanda yake ji an aiwatar da wani aiki a yankinsa da bai gamsu da shi ba.

Akwai kuma kwamitin da zai yi bincike a kan rikice-riciken siyasa da mutanen da suka ɓata da tashin hankalin da aka yi a 2015 da 2019 da kuma 2023.

Kafa wannan kwamatocin bincike dai ya haifar da ce-ce-ku-ce da kace-na-ce tsakanin ɓangaren tsohon gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje da kuma gwamnatin NNPP, inda bangaren Gandujen ke zargin akwai bita-da-ƙulli a binciken da ake ƙoƙarin yi, kasancewar an zaɓi tsohon gwamna ɗaya ne wajen yin binciken, zargin da gwamnatin kwankwasiyya ta musanta.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp