Rundunar Sojojin Nijeriya zata hukunta sojojin da suka hari a Tudun Biri

Shalkwatar tsaron Nijeriya ta ce sojojin da aka samu da laifi a kai hari kan masu mauludi a kauyen tudun biri na Jihar Kaduna zasu gurfana a gaban kotun hukunta sojoji domin fuskantar hukunci.

Daraktan yaɗa labarai na hedikwatar tsaron, Edward Buba ne ya bayyana haka a taron yaɗa labaran da aka gudanar a Abuja.

inda yace Hedikwatar tsaron ta kammala binciken da aka daɗe ana dako kan bam ɗin da aka jefa kan mutane a ƙauyen Tudun Biri dake a ƙaramar hukumar Igabi da ke jihar Kaduna.

A Disambar bara ne wani jirgin sojoji ya jefa bam kan mutanen da ke bikin maulidi lamarin da ya janyo asarar rayuka da jikkatar wasu da dama.

Rundunar sojin Najeriya ta ɗauki alhakin kai harin inda ta ce lamarin ya faru bisa kuskure.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 32 minutes 9 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 11 hours 13 minutes 34 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com