Home DUNIYA Kasar Benin ta dakatar da fitar da man fetur din Nijar ta...

Kasar Benin ta dakatar da fitar da man fetur din Nijar ta cikinta

Kasar Benin ta dauki matakin hana fitar da man da ake fitarwa daga Nijar ta hanyar bututun mai da ya hada rijiyoyin mai na Nijar ta tashar ruwan Cotonou.

Wannan matakin martani ne kai tsaye ga Nijar, wadda ke ci gaba da rufe kan iyakarta da Benin, duk da cewa Ƙungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka (ECOWAS) ta ɗage takunkumin da ta kakaba wa gwamnatin Nijar.

Sakamakon haka, ayyukan jiragen ruwa da aka keɓe don jigilar mai a halin yanzu ya tsaya cak.

An sanar da jakadan kasar China da ke kasar Benin, Peng Jingtao, tare da hukumar kula da bututun mai, Wapco, a hukumance kan wannan takunkumin.

Ana gudanar da hada-hadar da ta kai na kuɗi sama da CFA biliyan 600 ta hanyar bututun man na Nijar wanda ya ratsa ta cikin ƙasar Benin.

Gamayyar kamfanonin kasar Sin ne suka samar da bututun man mai tsawon kilomita 2,000 da kuma rijiyoyin mai na kasar Nijar.

An kammala aikin bututun man fetur ɗin wanda ake sa ran zai rika jigilar ganga 90,000 na mai a kowace rana zuwa tashar fitar da kaya a kasar Benin a farkon wannan shekarar.

Sai dai kuma rashin jituwar da ke tsakanin ƙasashen biyu bayan juyin mulkin watan Yulin 2023 da ya hambarar da shugaba Mohamed Bazoum na iya kawo cikas ga aikin.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp