Home DUNIYA Kasar Benin ta dakatar da fitar da man fetur din Nijar ta...

Kasar Benin ta dakatar da fitar da man fetur din Nijar ta cikinta

Kasar Benin ta dauki matakin hana fitar da man da ake fitarwa daga Nijar ta hanyar bututun mai da ya hada rijiyoyin mai na Nijar ta tashar ruwan Cotonou.

Wannan matakin martani ne kai tsaye ga Nijar, wadda ke ci gaba da rufe kan iyakarta da Benin, duk da cewa Ƙungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka (ECOWAS) ta ɗage takunkumin da ta kakaba wa gwamnatin Nijar.

Sakamakon haka, ayyukan jiragen ruwa da aka keɓe don jigilar mai a halin yanzu ya tsaya cak.

An sanar da jakadan kasar China da ke kasar Benin, Peng Jingtao, tare da hukumar kula da bututun mai, Wapco, a hukumance kan wannan takunkumin.

Ana gudanar da hada-hadar da ta kai na kuɗi sama da CFA biliyan 600 ta hanyar bututun man na Nijar wanda ya ratsa ta cikin ƙasar Benin.

Gamayyar kamfanonin kasar Sin ne suka samar da bututun man mai tsawon kilomita 2,000 da kuma rijiyoyin mai na kasar Nijar.

An kammala aikin bututun man fetur ɗin wanda ake sa ran zai rika jigilar ganga 90,000 na mai a kowace rana zuwa tashar fitar da kaya a kasar Benin a farkon wannan shekarar.

Sai dai kuma rashin jituwar da ke tsakanin ƙasashen biyu bayan juyin mulkin watan Yulin 2023 da ya hambarar da shugaba Mohamed Bazoum na iya kawo cikas ga aikin.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp