Home DUNIYA Mutum 44 sun kamu da cutar kwalara a Kenya sakamakon ambaliyar ruwa

Mutum 44 sun kamu da cutar kwalara a Kenya sakamakon ambaliyar ruwa

An samu rahoton mutum 44 sun kamu da cutar kwalara a lardin Tana River da ke Kenya yayin da ambaliyar ruwa ke ƙara buɗe ƙofar yaɗuwar cututtukan da ake iya ɗauka ta ruwa.

Sanarwa da Hukumar lafiya ta duniya ta fitar wadda ta bayyana adadin, inda ta ce hukumomi a Kenya tare da goyon bayan WHO da kuma sauran hukumomi na sa ido a kan cutar da matakan da za a ɗauka a faɗin ƙasar yayin da ake fama da ambaliyar.

Ambaliyar ta shafi kashi ɗaya cikin huɗu na mutane miliyan ɗaya tare da samun rahoton mutuwar mutum 238 a faɗin ƙasar. Tana River na ɗaya daga cikin lardunan da ambaliyar ta fi shafa a Kenya.

A ranar Talata ne babbar sakatariyar lafiya ta Kenya Mary Muthoni ta ce akwai babbar barazana na yiwuwar cututtukan da ke yaɗuwa ta ruwa su zama annoba idan ba a ɗauki mataki da wuri ba.

Ms Muthoni ta yi magana ne yayin da ita da sauran jami’an lafiya suke raba kayayyakin tsabtace ruwa a babban birnin Nairobi.

Ta kuma yi magana a kan haɗarin cututtukan da ake samu a lalataccen abinci da abincin da aka samu daga hanyoyi marasa nagarta da ambaliyar ta janyo ƙaruwarsu.

WHO ta ce za ta ci gaba da ba da goyon baya ga matakan gaggawa na gwamnati kuma za ta “ci gaba da sa ido kan ɓarkewar cututtuka da ka iya saurin yaɗuwa idan ba a yi saurin magance su ba”.

Ta kuma ce, “WHO ta kuma samar da kayayyakin magance cutar ta kwalara da ake rarrabawa a muhimman larduna wanda za su iya warkar da mutum 10,000”.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp