Home General NLC ta bawa Gwamantin Nijeriya Karshen watan Mayu

NLC ta bawa Gwamantin Nijeriya Karshen watan Mayu

Kungiyar Kwadago a Najeriya ta bai wa gwamnatin ƙasar nan karshen watan Mayu ta ƙara fito da sabon albashi mafi ƙaranci ga ma’aikatan ƙasar.

Ƙungiyar ta sanar da haka ne yayin bikin murnar ranar ma’aikata ta ƙasa a filin taron Eagle Square da ke Abuja a ranar Laraba.

Shugaban ƙungiyar NLC Joe Ajaero tare da takwaransa na ƙungiyar TUC Festus Osifo sun haɗu kan cewa mafi ƙaranci albashi na naira 30,000 ya yi wa ma’aikatan Najeriya kaɗan duba da yanayin matsi da kuma tsadar rayuwa da ya haɗa da tashin farashin abinci da kuɗin wuta da na sufuri da kuma sauransu.

Sun dage kan naira 615,000 a matsayin albashi mafi ƙaranci da suke so gwamnatin shugaba Bola Tinubu ta saka hannu kafin ƙarshen watan Mayun.

Ajaero ya ce, “Kungiyar NLC da ta TUC na jaddada cewa matsawar za a ci gaba da tattaunawa kan batun mafi ƙarancin albashi ba tare da mafita ba har zuwa ƙarshen Mayu ba za mu iya ci gaba da ba da haɗin kai ba a ƙasar nan”.

A ɓangaren Osifo kuma ya nemi hukumar kula da wutar lantarki tare da kamfanonin da suke rarraba wutar kan su janye ƙarin kuɗin da su ka yi wa mutane da ke rukunin A waɗanda suka fi samun wuta.

wannan dai na zuwa ne daidai lokacin da gwamnatin kasar karkashin shugaban Bola Tinubu ta furta batun karin ALbashin ga ma’aikatan kasar da kaso 25 da kuma 35 cikin dari, abinda kungiyoyin kwadagon ke kallon matsayin tufka da warwara.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp