Home Labarai An samar da ‘yan sanda da za suyi gadin makarantu a jihar...

An samar da ‘yan sanda da za suyi gadin makarantu a jihar Kano

Rundunar Yan Sandan Jihar Kano ta Samar da wata runduna ta musamman da zata Sanya Idanu akan Makarantun Dake Jihar Kano

Kwamishinan Yan Sandan Jihar Kano CP. Muhammad Ussaini Gumel shine ya Kaddamar da Rundunar a shelkwatar Yan Sandan Dake unguwar bompai a jihar

Aikin Rundunar shine Tabbatar da Tsaro a Makarantun da ake dasu a Kano, da Kuma Kai Dauki a duk Lokacin da aka Bukaci Hakan.

A cewar kwamishinan Yan Sandan Matakin Samar da Wannan rundunar, ya biyo bayan Umarnin Babban Sifetan Yan Sandan Nigeria Kayode Egbetokun, da ya Bukaci kowane kwamishinan Yan sanda ya Samar da irin Wannan runduna Domin baiwa Makarantun kariya

Haka kuma ya Bukaci Jami’an da aka zabo, suka Kuma samu horo da Suyi Aiki Tukuru Wajen Sauke Nauyin da aka Dora Musu, na kare lafiya da dukiyoyin al’umma

Jami’an zasuyi aiki kafada da kafada da Sauran Baturen Yan Sandan Dake Shiyyar da aka Tura su Domin aiki tare.

Haka Kuma an Samar da Motoci da Babura ga Jami’an Yan Sandan da zasuyi Wannan aiki na Tabbatar da Tsaro a Makarantun Dake Jihar Kano.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp