Home Labarai An samar da ‘yan sanda da za suyi gadin makarantu a jihar...

An samar da ‘yan sanda da za suyi gadin makarantu a jihar Kano

Rundunar Yan Sandan Jihar Kano ta Samar da wata runduna ta musamman da zata Sanya Idanu akan Makarantun Dake Jihar Kano

Kwamishinan Yan Sandan Jihar Kano CP. Muhammad Ussaini Gumel shine ya Kaddamar da Rundunar a shelkwatar Yan Sandan Dake unguwar bompai a jihar

Aikin Rundunar shine Tabbatar da Tsaro a Makarantun da ake dasu a Kano, da Kuma Kai Dauki a duk Lokacin da aka Bukaci Hakan.

A cewar kwamishinan Yan Sandan Matakin Samar da Wannan rundunar, ya biyo bayan Umarnin Babban Sifetan Yan Sandan Nigeria Kayode Egbetokun, da ya Bukaci kowane kwamishinan Yan sanda ya Samar da irin Wannan runduna Domin baiwa Makarantun kariya

Haka kuma ya Bukaci Jami’an da aka zabo, suka Kuma samu horo da Suyi Aiki Tukuru Wajen Sauke Nauyin da aka Dora Musu, na kare lafiya da dukiyoyin al’umma

Jami’an zasuyi aiki kafada da kafada da Sauran Baturen Yan Sandan Dake Shiyyar da aka Tura su Domin aiki tare.

Haka Kuma an Samar da Motoci da Babura ga Jami’an Yan Sandan da zasuyi Wannan aiki na Tabbatar da Tsaro a Makarantun Dake Jihar Kano.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp