Home Labarai An samar da ‘yan sanda da za suyi gadin makarantu a jihar...

An samar da ‘yan sanda da za suyi gadin makarantu a jihar Kano

Rundunar Yan Sandan Jihar Kano ta Samar da wata runduna ta musamman da zata Sanya Idanu akan Makarantun Dake Jihar Kano

Kwamishinan Yan Sandan Jihar Kano CP. Muhammad Ussaini Gumel shine ya Kaddamar da Rundunar a shelkwatar Yan Sandan Dake unguwar bompai a jihar

Aikin Rundunar shine Tabbatar da Tsaro a Makarantun da ake dasu a Kano, da Kuma Kai Dauki a duk Lokacin da aka Bukaci Hakan.

A cewar kwamishinan Yan Sandan Matakin Samar da Wannan rundunar, ya biyo bayan Umarnin Babban Sifetan Yan Sandan Nigeria Kayode Egbetokun, da ya Bukaci kowane kwamishinan Yan sanda ya Samar da irin Wannan runduna Domin baiwa Makarantun kariya

Haka kuma ya Bukaci Jami’an da aka zabo, suka Kuma samu horo da Suyi Aiki Tukuru Wajen Sauke Nauyin da aka Dora Musu, na kare lafiya da dukiyoyin al’umma

Jami’an zasuyi aiki kafada da kafada da Sauran Baturen Yan Sandan Dake Shiyyar da aka Tura su Domin aiki tare.

Haka Kuma an Samar da Motoci da Babura ga Jami’an Yan Sandan da zasuyi Wannan aiki na Tabbatar da Tsaro a Makarantun Dake Jihar Kano.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp