Home Labarai Najeriya ta magantu kan zargin neman cin hanci daga kamfanin Binance

Najeriya ta magantu kan zargin neman cin hanci daga kamfanin Binance

Gwamnatin Najeriya ta musanta iƙirarin da kamfanin hada-hadar kuɗi ta intanet, Binance ya yi kan cewa wani jami’in gwamnatin ƙasar ya nemi cin hanci daga jami’in kamfanin na kuɗin kirifto dala miliyan 150.

Ta cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun mai magana da yawun ministan yaɗa labari na Najeriya hannun Rabi’u Ibrahim, ta ce zargin na kamfanin Binance wani yunƙuri ne na “ɓata wa Najeriya suna domin ɓoye ayyukan da yake yi na saɓa ƙa’ida”.

Sanarwar ta ce “babu ko ƙwayar zarra ta gaskiya a zargin da kamfanin na Binance ya yi.”

A ranar Talata ne shugaban kamfanin na Binance, Richard Teng ya yi zargin, wanda aka wallafa a jaridar New York Times ta Amurka da ma wasu jaridun duniya a ci gaba da taƙaddamar da ake yi tsakanin kamfanin na kuɗin kirifto da Najeriya.

Sanarwar ta ci gaba da cewa gaskiyar lamarin shi ne ana ci gaba da tuhumar Binance a Najeriya saboda barin da ya yi aka yi amfani da shafinsa wajen “halasta kuɗaɗen haram da taimaka wa ayyukan ta’addanci da kuma ƙayyade farashin kuɗin ƙasashen ƙetare ba bisa ƙa’ida ba”.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp