Yajin aikin da ƴan kwadago ke yi ya saɓa wa doka – Gwamnatin Najeriya

Ministan shari’a na Najeriya Lateef Fagbemi ya ce yajin aikin da manyan ƙungiyoyin ƙwadagon ƙasar suka fara a ranar litinin kan mafi ƙanƙantar albashi ya saɓa wa doka.

Babban lauyan na gwamnati ya bayyana hakan ne bisa dalilin cewa ƙungiyoyin ba su bi ka’idojin da dokar ƙwadago ta gindaya ba.

wannan dai na zuwa ne bayan manyan kungiyoyin ma’aikata biyu na NLC da TUC, suka fara yajin aikin sai baba-ta-gani daga Litinin bayan gwamnati ta gaza cika wa’adin ranar 31 ga watan Mayu na aiwatar da ƙarin albashi mafi ƙanƙanta da kuma rage farashin wutar lantarki.

Ƙungiyar ƙwadago ta Najeriya ta NLC da TUC sun ce za a fara yajin aikin har sai sun sami sabon albashi mafi ƙanƙanta na ƙasa kuma har sai gwamnati ta yi da gaske.

Ƙungiyoyin ƙwadagon na son a sanya albashi mafi ƙanƙanta kan dala $334, kwatankwacin N494,000 kenan inda kuma gwamnati ta tsaya a kan Naira 30,000, kwatankwacin dala 22, duk wata.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 30 minutes 21 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 11 hours 11 minutes 46 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com