Home General Gwamnatin Kano ta zargi Kwamishinan ‘Yan Sandan jihar.

Gwamnatin Kano ta zargi Kwamishinan ‘Yan Sandan jihar.

Gwamnatin jihar Kano ta zargi rundunar ‘yan Sandan jihar da daukar bangaranci a rikincin Masarautar dake faruwa a jihar.

Daraktan yada labaran Gwamnan jihar Sunusi Bature Dawakin Tofa ne ya bayyana hakan ta cikin wata hira da tashar Talabijin ta Channels a cikin shirin Politics Today na ranar Juma’a.

Idan za’a iya tunawa tun bayan da majalisar jihar kano ta yiwa dokar masarautar jihar gyaran fuska, gwamnan jihar ya umarci kwamishinan ‘yan sandan daya fidda tsohon sarki Aminu Ado bayero daga fadar sarkin ta gidan Rumfa.

Sai dai rundunar ‘yan sandan bisa jagoranci CP Usaini Gumel tayi fatali da umarnin gwamnan inda tace umarnin kotu yafi dacewa ta bi.

Ta cikin ganawar Sunusi Bature ya bayyana cewa hukuncin Kotun tarayya su ya bawa nasara domin kuwa kotun bata rushe dokar data sauke tsoffin sarakunan jihar guda biyar ba.

Daga bisani Dawakin Tofa ya bayyana muhimmancin dawo da martabar sarautar kano da ya zargi tsohuwar Gwamnatin Ganduje da kassarawa.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp