Home DUNIYA NCDC ta ce bata da wadatacciyar Allurar Rigakafin Kwalara

NCDC ta ce bata da wadatacciyar Allurar Rigakafin Kwalara

Hukumar dake dakile yaduwar cuttukka ta Nijeriya NCDC tace bata da wadatacciyar Allurar ragakafin cutar kwalara.

Daraktan hukumar Dr. Jide Idris ne ya bayyana hakan, inda yace kasar ta bayar da sallahun allurar ga hukumomin dake da alhakin sayar da ita a duniya da masu bayar da tallafinta, duk da cewa bai bayyana ranar da allurar zata iso ba.

Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da rahotannin ke bayyana yadda mutane 40 suka mutu sakamakon kamuwa da cutar ta kwalara a kasar nan.

Dr. Jide ya bukaci al’ummar kasar nan da su yi amfani da allurer rigakafin da wasu matakan kariya daga kamuwa da cutar ta kwalara.

Cutar kwalara dai na guda cikin cututtukan da ake daukar su ta hanyar shan ruwa ko abinci maras tsafta, wanda takan kai ga hallaka mutun bayan kamuwa da ita.

Bincike dai ya nuna cewa a cikin shekaru hudu da suka gabata cutar ta hallaka mutane 4,364 yayin da aka zargi mutane 139,730 da suka kamu da cutar a kasar nan.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban JosMatsalar Tsaro:  An Kashe Manoma 6 a Jihar Kaduna An Zargi Kwankwaso da Sayen Fom ɗin Takara na Kujeru 69 a Jam'iyyar PRPƘasurgumin ɗan bindiga, Turji ya ɗauki Alhakin Kashe Sojoji a Jihar SokotoMasu Iƙirarin Jihadi Sun Hallaka Manoma 11 a Jihar Borno 'Yan Bindiga sun ƙone shingen Jami'an NSCDC Tare da Garkuwa da Mutum 1 a Jihar KebbiTaron NUJ: Lokacin Da Manyan Jami’an Tsaro Suka Guji Yan Jarida Daga Yushau A. ShuaibSamar da Tsaro: Sojojin Najeriya sun Kama ƴan ƙasashen Wajen 46Ta'addanci: Za a Gurfanar da Mutane 400 a Gaban Kotun Tarayya da ke AbujaAn Ceto Matar Janar Rabe da ya Rasu a Hannun ƴan BindigaHauhawar Farashin Kayan Masarufi a Najeriya ya ƙaru Zuwa Kashi 15.93Rundunar Sojin Najeriya ta Gudanar da Hare-Hare Kan Maɓoyar ƴan Bindiga a Jihar Katsina
X whatsapp