Home DUNIYA Gwamnatin Jihar Sokoto ta Musanta yunkurin cire Sarkin Musulmi

Gwamnatin Jihar Sokoto ta Musanta yunkurin cire Sarkin Musulmi

Gwamnatin jihar Sokoto ta musanta zargin cire mai alfarma sakin musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar III,

Wannan na cikin wata sanar wada mai Magana da yawun Gwamnan jihar Abubakar Bawa ya fita aka raba ta ga manema labarai, sanarwar kuma bukaci Mataimakin Shugaban ƙasa Kashim Shettima ya rika bincike kafin yin sharhi kan duk Wani Labari da ya gani a kafofin sadarwa na zamani.

“Munyi zaton mataimakin shugaban kasa ya tuntubi Gwamnan Jihar sokoto kafin ya fito fili yayi magana akan Batun Tsige Sarkin Musulmi.

“gaskiyar magana ita ce, ba’a taba yunkurin tsige Sarkin ba, haka kuma ba mu aika masa da wata barazana ba dangane da hakan ba a cewar Sanarwar”

Sanarwar ta kara da cewa, Sarkin Musulmi na cin moriyar duk wani ikon da yake da shi, ba mu taba tauye masa wani ‘yanci ko hakkinsa ba”

Haka Gwamnati da al’ummar Jihar Sokoto na girmama Majalisar Sarkin Musulmi kuma zasu yi duk mai yiwuwa don kare martabar wannan Masarautar”.

“Daga bisani gwamnati na tabbatarwa ‘yan Nijeriya cewa, za ta cigaba da kare Majalisar Sarkin Musulmi da mutuncinta a kowane lokaci”

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp