Home DUNIYA Gwamnatin Jihar Sokoto ta Musanta yunkurin cire Sarkin Musulmi

Gwamnatin Jihar Sokoto ta Musanta yunkurin cire Sarkin Musulmi

Gwamnatin jihar Sokoto ta musanta zargin cire mai alfarma sakin musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar III,

Wannan na cikin wata sanar wada mai Magana da yawun Gwamnan jihar Abubakar Bawa ya fita aka raba ta ga manema labarai, sanarwar kuma bukaci Mataimakin Shugaban ƙasa Kashim Shettima ya rika bincike kafin yin sharhi kan duk Wani Labari da ya gani a kafofin sadarwa na zamani.

“Munyi zaton mataimakin shugaban kasa ya tuntubi Gwamnan Jihar sokoto kafin ya fito fili yayi magana akan Batun Tsige Sarkin Musulmi.

“gaskiyar magana ita ce, ba’a taba yunkurin tsige Sarkin ba, haka kuma ba mu aika masa da wata barazana ba dangane da hakan ba a cewar Sanarwar”

Sanarwar ta kara da cewa, Sarkin Musulmi na cin moriyar duk wani ikon da yake da shi, ba mu taba tauye masa wani ‘yanci ko hakkinsa ba”

Haka Gwamnati da al’ummar Jihar Sokoto na girmama Majalisar Sarkin Musulmi kuma zasu yi duk mai yiwuwa don kare martabar wannan Masarautar”.

“Daga bisani gwamnati na tabbatarwa ‘yan Nijeriya cewa, za ta cigaba da kare Majalisar Sarkin Musulmi da mutuncinta a kowane lokaci”

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp