Home DUNIYA Kotu a Abuja ta dage saurarar karar da ake bukatar Ganduje ya...

Kotu a Abuja ta dage saurarar karar da ake bukatar Ganduje ya sauka daga shugabancin APC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja a Najeriya ta sake dage sauraren karar da ke neman a tsige tsohon gwamnan jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje a matsayin shugaban jam’iyyar APC na kasar har zuwa ranar 5 ga watan Yuli.

Mai shari’a Inyang Ekwo, a ranar Laraba, ya dage ci gaba da zama sauraron karar a karo na biyu domin baiwa mai kara damar amsa sabuwar bukatar da Ganduje ya shigar na kalubalantar cancantar karar.

A zaman na Laraba, lauyan mai kara, Benjamin Davou, ya shaida wa kotun cewa Sanusi Musa, SAN, wanda ke kare Ganduje, ya mika masa wata sabuwar bukata.

Ya ce zai bukaci lokaci don yin nazari kan ko zai amsa takardar. Lauya Musa bai yi adawa da bukatar Davou na dage zaman ba.

A saboda haka mai shari’a Ekwo ya dage ci gaba da sauraron karar har sai ranar 5 ga watan Yuni domin ci gaba.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp