Kotu a Abuja ta dage saurarar karar da ake bukatar Ganduje ya sauka daga shugabancin APC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja a Najeriya ta sake dage sauraren karar da ke neman a tsige tsohon gwamnan jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje a matsayin shugaban jam’iyyar APC na kasar har zuwa ranar 5 ga watan Yuli.

Mai shari’a Inyang Ekwo, a ranar Laraba, ya dage ci gaba da zama sauraron karar a karo na biyu domin baiwa mai kara damar amsa sabuwar bukatar da Ganduje ya shigar na kalubalantar cancantar karar.

A zaman na Laraba, lauyan mai kara, Benjamin Davou, ya shaida wa kotun cewa Sanusi Musa, SAN, wanda ke kare Ganduje, ya mika masa wata sabuwar bukata.

Ya ce zai bukaci lokaci don yin nazari kan ko zai amsa takardar. Lauya Musa bai yi adawa da bukatar Davou na dage zaman ba.

A saboda haka mai shari’a Ekwo ya dage ci gaba da sauraron karar har sai ranar 5 ga watan Yuni domin ci gaba.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1189 days 15 hours 18 minutes 48 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1171 days 17 hours 13 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com