Home General Gwamantin Kano zata cigada da ayyukan da kwankwaso ya fara

Gwamantin Kano zata cigada da ayyukan da kwankwaso ya fara

Gwamnatin jihar Kano ta kammala shirin kammala aiyukan titinan karkara mai tsawon kilomita 5 da aka yi watsi da shi a fadin kananan hukumomi 44 na jihar.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ne ya ba da wannan tabbacin ne a ranar Laraba bayan kammala wani taro da ‘yan kwangilar da ke gudanar da ayyukan a gidan gwamnati.

Ayyukan na kilomita biyar-biyar da aka warewa miliyoyin nairori tsohon gwamna, Dr. Rabiu Musa Kwankwaso ne ya bayar da su a lokacin gwamnatin sa, kuma tsohuwar gwamnatin Abdullahi Umar Ganduje ta yi watsi da su.

Da yake ganawa da ‘yan kwangilar, Gwamna Yusuf ya yabawa musu kan yadda suka amsa kira a kan lokaci, ya kuma ba da tabbacin gwamnatinsa ta kudirci aniyar kammala duk ayyukan da tsohuwar gwamnatin Kwankwaso ta faro don cigaba al’ummar jihar Kano.

Muhimman batutuwan da aka cimma yayin taron sun hada da Komawar yan kwangilar baki aiki nan da mako guda don kammala aikin.

Sauran su ne umarnin gaggawa da aka baiwa ma’aikatar filaye da tsare-tsare ta Jihar domin warware matsalolin da ake fuskanta na biyan diyya.

“An yanke shawarar cewa ‘yan kwangilar za su je bankunan su domin karbar kashi 30 cikin 100 na kudaden da aka ware wa aikin, amma ga wadanda basu karɓi na su tun da farko ba.

“An kuma warware matsalar hauhawar farashin kayayyakin gine-gine da aka samu, inda gwamnati ta amince za ta sake duba farashin sauran kayayyakin da aike aikin da su .

“An kuma amince da cewa gwamnati za ta fitar da tsarin da zata rika biyan yan kwangilar a kowane wata, ta yadda ba za sami tsaiko ba. Don haka aka umarci duk dan kwangilar da ya amince da sabon tsarin da ya koma bakin aiki nan da mako guda ko ya rasa damar”.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp