NDLEA ta Bukaci yin Gwajin shaye-shaye kafin Aure a jihar Kano

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta Nijeriya NDLEA reshen jihar Kano ta bukaci wajabta yin gwajin ta’ammali da miyagun kwayoyi kafin aure a jihar.

Kwamandan hukumar  Abubakar Idris Ahmad ne ya bayyana hakan yayin da yake ganawa da kamfanin dillancin labarai na Nijeriya (NAN) a ranar Alhamis.

“A yunkurin hukumar na dakile dabiar ta’ammali da miyagun kwayoyi ta gabatar da wannan gwaji don kawar da dabiar daga Nijeriya,” a cewar sa.

Idris Ahmad yace gwajin zai zama wani mataki na magance shan miyagun kwayoyin da kuma kare wadanda basu fara ba daga cikin ma’auratan gami da wayar da kai da fadakar da su hadarin fadawa harkokin shaye – shayen.

Ya ce samar da dokar zai taimaka matuka wajen magance yawan mutuwar aure, gami da rage yawan matan aure dake shiga harkokin shaye – shayen a jihar.

daga bisani kwamandan hukumar ya bukaci wata da matasa da su guji dabi’ar shaye – shaye tare da bata hadin kai don kawar da ta’adar daga jihar da kasa baki daya.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 22 minutes 31 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 11 hours 3 minutes 56 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com