Sojojin saman Nijeriya sun hallaka Mayakan Boko Haram 7 a Jihar Borno

Sojojin saman Nijeriya dake karkashin Operation Hadin kai sun sami nasarar hallaka ýan Ta’adda 7 a jihar Borno dake arewa maso gabashin Nijeriya.

wanna na cikin wata sanrwa da darakta yada labarai da hulda da jama’a na rundunar AVM Edward Gabkwet ya fitar ranar alhamisa a birnin tarayya Abuja.

Gabkwet ta cikin sanarwar yace dakarun sun sami nasarar ne bayan farwa maboyar ‘yan ta’addan dake tsaunikan Degbewa da Chinene dukkan su a Mandara.

Ya kara da cewa kafin dakarun sojin saman su kai harin sai da suka gudanar bincike gami da sintiri a yankunan na tsahon kwanaki, wanda ya hadar da tantance adadin ‘yan ta’addan dake rayuwa a wurin.

Ya kuma ce ana zargin wajen matsayin wani wuri na hada abubuwan fashe da killace su.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1485 days 18 hours 25 minutes 7 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1467 days 20 hours 6 minutes 32 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com