Home DUNIYA Kada ku bari ’yan ta’adda su kassara zaman lafiyar kasar nan –...

Kada ku bari ’yan ta’adda su kassara zaman lafiyar kasar nan – Tinubu ga sojoji

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, ya bukaci dakarun sojoji da kada su bari ’yan ta’adda su ga bayan al’ummar Nijeriya.

Tinubu ya bayyana hakan ne a ranar Asabar a wani bangare na bikin da rundunar sojin ta gudanar a barikin sojoji na uku da ke Rukuba a Karamar Hukumar Bassa a jihar Filato.

Tinubu wanda ya sami wakilcin Ministan Tsaro, Alhaji Badaru Abubakar, ya ce wajibi dakarun su kare rayukan ’yan kasar a gidaje ko kuma a wuraren mu’amalarsu na yau da kullum.

da yake bayani tun da farko, Babban Hafsan Sojojin Nijeriya, Laftanar Janar Taoreed Lagbaja, ya ce sojojin kasar nan kwararru ne tsahon shekaru 161.

Nijeriya dai na fama da matsalolin rashin tsaro wacce ta addabi Arewacin kasar, yayin da na kudanci ke fama da matsaloli barayin mai da masu kokarin ficewa daga ƙasar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp