Home DUNIYA Dalilin Gwamnatin Nijeriya na dakadar da biyan haraji kan kayan Abinci

Dalilin Gwamnatin Nijeriya na dakadar da biyan haraji kan kayan Abinci

Gwamnatin Nijeriya ta cire harajin da dukkannin wasu kunji-kunji kan kayan kayan abincin da zaá shigo da su kasar.

wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da ministan noma da samar da wadataccen abinci Abubakar Kyari ya sanyawa hannun a ranar litinin.

abincin da sanarwar ta lisafta sun hadar da samfarerar shinkafa, masara, alkama da kuma tsabar wake.

yace dakatar da biyan harajin na matsayin wani mataki cikin matakan da gwamnati zata dauka nan da kanaki 180 masu zuwa na kawar da matsalar tsadar abinci a kasar.

Ya ce shugaba Tinubu ya amince da janye kudin fito kan muhimman kayan abincin ne har tsawon kwanaki 150, domin saukaka tsadar kayayyakin abinci da ake fama da su.

Ministan, ya bayyana irin ƙoƙarin da Gwamnatin Tarayya ke yi na yaƙi da hauhawar farashin kayan abinci.

Tsada da matsin rayuwa ya ƙaru tun bayan da Shugaba Tinubu ya hau kan karagar mulki a ranar 29 ga watan Mayun 2023.

Gwamnati za ta shigo da alkama da masara daga waje, Sanarwar ta ce baya ga janye ƙuɗin fito ga ’yan kasuwa masu buƙatar shigo da kayan abinci.

Har wa yau, Gwamnatin Tarayya za ta shigo da alkama kimanin tan dubu 250 da masara tan 250 da za ta bai wa kamfanoni jihohi da ke sarrafa su.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp