Home DUNIYA Majalisar wakilai ta bukaci a gaggauta dakarar da yarjejeniyar Samoa

Majalisar wakilai ta bukaci a gaggauta dakarar da yarjejeniyar Samoa

Majalisar Wakilan Nijeriya ta bukaci gwamnatin Tarayya ta yi gaggawar dakatar da yarjejeniyar SAMOA da ta haifar da cece-kuce da zargin taba martabar addini da al’adun mutanen Nijeriya.

Majalisar ta kuma yanke shawarar bincikar yarjejeniyar da gwamnatin tarayya ta rattabawa hannu a ranar 28 ga watan Yuni.

An zartar da kudurin ne biyo bayan amincewa da kudirin gaggawa na Ali Sani Madaki,  sashin  marasa rinjaye, da wasu ‘yan majalisa 87 suka dauki nauyi.

Kwanan nan yarjejeniyar ta haifar da cece-kuce saboda rahotannin cewa an shigar da tanade-tanade da suka shafi ‘yan madigo, ‘yan luwadi, bisexual, da transgender (LGBT) a cikin yarjejeniyar.

sai dai wannan na zuwa ne daidai lokacin da kungiyar lauyoyin kasar ta NBA da ake kallon matsayin masana doka suka fitar da sanarwar dake cewa cikin yarjejeniyar babu wani batun auren jinsi ko makamantan sa.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp