Home DUNIYA Babu batun ‘yancin Madigo, Luwadi, Bisexual, Transgender da Queer (LGBTQ) – Samoa

Babu batun ‘yancin Madigo, Luwadi, Bisexual, Transgender da Queer (LGBTQ) – Samoa

Kungiyar Lauyoyin Nijeriya ta NBA ta ce a cikin yarjejeniyar Samoa babu wani abu da ya tilastawa Najeriya amincewa da ‘yancin ‘yan Madigo, Luwadi, Bisexual, Transgender da Queer (LGBTQ).

Shugaban kungiyar Mista Yakubu Maikyau (SAN), ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun sakataren yadda labaran Kungiyar NBA na kasa, Mista Habeeb Lawal, Maikyau ya yi gargadi game da munanan labaran da ke tasowa daga bayanan karya kan yarjejeniyar.

Ya ce: “ Hankalina ya karkata ga yadda ake buga jaridu da kafafen sada zumunta na zamani, game da martanin da wasu ‘yan Najeriya suka yi, game da rattaba hannu kan yarjejeniyar SAMOA da gwamnatin tarayya ta yi.

 

“Sabanin labarin da ake yadawa ko dai saboda rashin sanin abin da yarjejeniyar ta kunsa ko kuma da gangan na yaudarar jama’a,.

“Wannan babu wani tanadi a cikin yarjejeniyar Samoa da ta bukaci Najeriya ta amince ko ta kowace hanya ta amince da LGBTQ ko ‘yan luwadi, ko dai a matsayin wani sharadi na bashi dala biliyan 150 ko kwata-kwata.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp