Masarautar Kano ta tabbatar da tashin gobara a fadar sarki Muhammadu Sunusi II

Masarautar Kano ta tabbatar faruwar gobara da ake zargin kunnata aka yi a fadar Sarkin Kano na Malam Muhammadu Sanusi na biyu.

A sanarwar da shugaban ma’aikatan Sarkin Kano, Munnir Sanusi Abbas ya fitar a yammacin wannan rana ya ce wutar ta tashi ne a safiyar Asabar.

Sanarwar ta ƙara da cewa, wutar wacce bata yi ɓarna mai yawa ba, ana kan binciken abinda ya haifar da ita.

A cewar sanarwar “Fadar na ɗaukar dukkan matakan da suka dace wajen tabbatar da tsaron fadar dama mutanen dake ciki, kuma tuni aka fara bincike don kaucewa tashin gobarar anan gaba”.

Tun da fari dai wani rahoto da ya fita a yammacin wannan rana ya ambaci rundunar ‘yan sanda jihar da tabbatar da aukuwar gobarar a fadar sarkin dake kofar kudu a gidan na rumfa.

Ko da dai itama rundunar bata ayyana musabban faruwar gobarar ba tace dai tana bincike ne kan abin da ya haddasa ta.

PRNigeria hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 33 minutes 57 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 11 hours 15 minutes 22 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com