Home General Kudurin kirkirar sarakuna 3 masu daraja ta 2 ya tsallake karatu a...

Kudurin kirkirar sarakuna 3 masu daraja ta 2 ya tsallake karatu a Majalisar Dokokin Kano

Majalisar jihar Kano
Majalisar jihar Kano

Kudurin kirkirar sarakuna masu daraja ta biyu ya tsallake karatun farko a majalisar dokokin Kano

Sabon kudurin ƙirƙirar sakaruna masu daraja ta biyu ya tsallake karatu na farko a zauren Majalisar Dokokin Jihar Kano.

Sabbin Sarakunan da aka ƙirƙira dai sune na Rano, Ƙaraye da kuma Gaya.

A cewar ƙudurin, dukkansu za su kasance ne ƙarƙashin Sarkin Kano, wanda shi kaɗai ne mai daraja ta ɗaya yanzu a jihar.

Kananan hukumomin da za su kasance ƙarƙashin Sarkin Rano sune Rano Kibiya da Bunkure, shi kuma na Karaye yana da kananan hukumomin Karaye da Rogo.

Matakin na zuwa ne bayan Majalisar ta rushe dokar da ta kirkiri sabbin masarautu guda biyar a jihar ta shekara ta 2019, tare da rushe sarakunan da aka naɗa musu.

Daga bisani dai Gwamnan Jihar, Abba Kabir Yusuf, ya dawo da Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II kan kujerarsa, inda ya sauke Aminu Ado Bayero da sauran sarakunan guda hudu.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp