Home General Masu garkuwa sun saki mahaifiyar mawaƙi Rarara

Masu garkuwa sun saki mahaifiyar mawaƙi Rarara

Mahaifiyar fitaccen mawaƙin nan na siyasa, Dauda Kahutu Rarara, wato Hajiya Halima Adamu, ta shaƙi iskar ’yanci bayan ’yan bindigar da suka yi garkuwa da ita sun sako ta.

Mawaƙi Rararan ne ya tabbatar da sakin nata a shafinsa na Instagram, inda ya ce an sako ta ne da sanyin safiyar Laraba.

Ya bayyana godiyarsa ga Allah sannan ya gode wa sauran jama’a kan gudunmawar addu’o’in da suka yi mata bayan faruwar lamarin.

Sai dai bai yi bayani kan ko an biya kudin fansa ba kafin sakin nata ko kuma a’a.

A baya dai, rahotanni sun bayyana cewar masu garkuwar sun buƙaci a ba su Naira miliyan 900 kafin su sake ta.

Tun kusan mako uku da suka gabata ne dai wasu ’yan bindiga da ba a san ko su wane ne ba suka sace Hajiya Halima mai kimanin shekaru 75 a gidanta da ke ƙauyen Kahutu a ƙaramar hukumar Ɗanja ta jihar Katsina.

Rarara dai ya yi suna wajen waƙe ’yan siyasa, musamman na jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya.

A lokuta da dama, ya sha nuna cewa gwamnatin APCn tana iya kokarinta wajen magance matsalar tsaron da ta addabi ƙasar, ciki har da ta ’yan bindiga da masu garkuwa da mutane.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp