Home General Fadar Shugaban kasa ta bayyana masu shirin rusa Nijeriya

Fadar Shugaban kasa ta bayyana masu shirin rusa Nijeriya

Fadar shugaban kasa ta zargi dan takarar shugaban kasa karkashin inuwar Jam’iyyar Labour Party Peter Obi da yunkurin kifar da gwamnatin Bola Tinubu.

Mataimaki na musamman ga shugaban Bola Tinubu kan harkokin yada labarai da dabaru, Bayo Onanuga ne ya bayyana hakan a shafinsa na x ranar asabar.

Ya ce akwai zargin magoya bayan Peter Obi, da yunkurin tsige shugaban kasa Bola Tinubu a shirin su na gudanar da wata zanga-zanga mako na sama.

To sai dai guda cikin dattijai a jam’iyyar ta Labour Dr. Chike obidigbo, ya bukaci shugaban kasa bola tinubu ya ja wa Bayo Onanuga kunne bisa yunkurin bisa kalaman da zai kai ga tarwatsa kasar nan.

Obidigbo yace abin takaici ne jin irin wadannan kalamai batanci daga bakin mai taimakawa shugaban kasa na musamman akan harkokin sadarwa, wanda zai kai ga hassalawa wand aba tarwatsawa Nijeriya kawai zai yi ba zai saka kasar nan ne cikin mawuyacin hali.

Bayan shekara guda na gwamnatin Shugaba Tinubu tayi, da yawa daga cikin sauye-sauyen tattalin arziki sun haifar da hauhawar farashin kayayyaki, musamman a bangaren da ya shafi abinci.

Da dama daga cikin yan kasar ne ke ci gaba da bayyana damuwa ganin halin matsin tattalin arziki da suka shiga.

Sai dai magoya bayan Shugaban kasar na ganin cewa Bola Tinubu na iya kacin kokarin sa wajen samnarwa yan kasar da ababen more rayuwa.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp