Home General ‘Yan sanda a Nijeriya sun kama mutane 1,284 da ake zargi da...

‘Yan sanda a Nijeriya sun kama mutane 1,284 da ake zargi da laifuka

Rundunar ‘yan sandan kasar nan ta ce dakarunta sun sami nasarar kama mutane 1,284 da ake zargi da aikata mabambanta laifuka a cikin makwannin shidda da suka gabata.

Mai Magana da yawun hukumar na kasa Muyiwa dejobi ne ya bayyana hakan a ranar Juma’a a yayin da ake holen wadanda ake zargin da aikata laifuka daban daban.

Haka kuma yace daga cikin wadanda aka kama akwai mutum 307 da ake zargin su da aikata fashi da makami sai kuma 296 da ake zargi da aikata laifukan garkuwa da mutane domin karbar kudin fansa, sai kuma mutane 176 da ake zargi da laifukan fyade da tabargaza, ana kuma zargi mutane 301 da aikata laifukan kisan kai, sai kuma mutane 204 da ake zargin su da shiga kungiyoyin asiri.

Adejobi yace rundunar ta sami nasarar kubutar da mutane 97 da akayi garkuwa da su, inda suka sami nasarar kwato makamai 284 gami da alburusai 6,702.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp