Home General ‘Yan sanda a Nijeriya sun kama mutane 1,284 da ake zargi da...

‘Yan sanda a Nijeriya sun kama mutane 1,284 da ake zargi da laifuka

Rundunar ‘yan sandan kasar nan ta ce dakarunta sun sami nasarar kama mutane 1,284 da ake zargi da aikata mabambanta laifuka a cikin makwannin shidda da suka gabata.

Mai Magana da yawun hukumar na kasa Muyiwa dejobi ne ya bayyana hakan a ranar Juma’a a yayin da ake holen wadanda ake zargin da aikata laifuka daban daban.

Haka kuma yace daga cikin wadanda aka kama akwai mutum 307 da ake zargin su da aikata fashi da makami sai kuma 296 da ake zargi da aikata laifukan garkuwa da mutane domin karbar kudin fansa, sai kuma mutane 176 da ake zargi da laifukan fyade da tabargaza, ana kuma zargi mutane 301 da aikata laifukan kisan kai, sai kuma mutane 204 da ake zargin su da shiga kungiyoyin asiri.

Adejobi yace rundunar ta sami nasarar kubutar da mutane 97 da akayi garkuwa da su, inda suka sami nasarar kwato makamai 284 gami da alburusai 6,702.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp