Home General Fadar Shugaban kasa ta bayyana masu shirin rusa Nijeriya

Fadar Shugaban kasa ta bayyana masu shirin rusa Nijeriya

Fadar shugaban kasa ta zargi dan takarar shugaban kasa karkashin inuwar Jam’iyyar Labour Party Peter Obi da yunkurin kifar da gwamnatin Bola Tinubu.

Mataimaki na musamman ga shugaban Bola Tinubu kan harkokin yada labarai da dabaru, Bayo Onanuga ne ya bayyana hakan a shafinsa na x ranar asabar.

Ya ce akwai zargin magoya bayan Peter Obi, da yunkurin tsige shugaban kasa Bola Tinubu a shirin su na gudanar da wata zanga-zanga mako na sama.

To sai dai guda cikin dattijai a jam’iyyar ta Labour Dr. Chike obidigbo, ya bukaci shugaban kasa bola tinubu ya ja wa Bayo Onanuga kunne bisa yunkurin bisa kalaman da zai kai ga tarwatsa kasar nan.

Obidigbo yace abin takaici ne jin irin wadannan kalamai batanci daga bakin mai taimakawa shugaban kasa na musamman akan harkokin sadarwa, wanda zai kai ga hassalawa wand aba tarwatsawa Nijeriya kawai zai yi ba zai saka kasar nan ne cikin mawuyacin hali.

Bayan shekara guda na gwamnatin Shugaba Tinubu tayi, da yawa daga cikin sauye-sauyen tattalin arziki sun haifar da hauhawar farashin kayayyaki, musamman a bangaren da ya shafi abinci.

Da dama daga cikin yan kasar ne ke ci gaba da bayyana damuwa ganin halin matsin tattalin arziki da suka shiga.

Sai dai magoya bayan Shugaban kasar na ganin cewa Bola Tinubu na iya kacin kokarin sa wajen samnarwa yan kasar da ababen more rayuwa.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp