Home General Fadar Shugaban kasa ta bayyana masu shirin rusa Nijeriya

Fadar Shugaban kasa ta bayyana masu shirin rusa Nijeriya

Fadar shugaban kasa ta zargi dan takarar shugaban kasa karkashin inuwar Jam’iyyar Labour Party Peter Obi da yunkurin kifar da gwamnatin Bola Tinubu.

Mataimaki na musamman ga shugaban Bola Tinubu kan harkokin yada labarai da dabaru, Bayo Onanuga ne ya bayyana hakan a shafinsa na x ranar asabar.

Ya ce akwai zargin magoya bayan Peter Obi, da yunkurin tsige shugaban kasa Bola Tinubu a shirin su na gudanar da wata zanga-zanga mako na sama.

To sai dai guda cikin dattijai a jam’iyyar ta Labour Dr. Chike obidigbo, ya bukaci shugaban kasa bola tinubu ya ja wa Bayo Onanuga kunne bisa yunkurin bisa kalaman da zai kai ga tarwatsa kasar nan.

Obidigbo yace abin takaici ne jin irin wadannan kalamai batanci daga bakin mai taimakawa shugaban kasa na musamman akan harkokin sadarwa, wanda zai kai ga hassalawa wand aba tarwatsawa Nijeriya kawai zai yi ba zai saka kasar nan ne cikin mawuyacin hali.

Bayan shekara guda na gwamnatin Shugaba Tinubu tayi, da yawa daga cikin sauye-sauyen tattalin arziki sun haifar da hauhawar farashin kayayyaki, musamman a bangaren da ya shafi abinci.

Da dama daga cikin yan kasar ne ke ci gaba da bayyana damuwa ganin halin matsin tattalin arziki da suka shiga.

Sai dai magoya bayan Shugaban kasar na ganin cewa Bola Tinubu na iya kacin kokarin sa wajen samnarwa yan kasar da ababen more rayuwa.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp