Home DUNIYA Biden ya janye daga takarar Shugabancin kasar Amurka

Biden ya janye daga takarar Shugabancin kasar Amurka

Shugaban kasar Amurka Joe biden ya dakatar da yakin neman zabensa a ranar lahadi.

wannan ya biyo bayan hukuncin da jam’iyyar sa ta demukrat ta yanke kan ingancin lafiyar kwakwalwarsa, da kuma binda take gani matsami nakasu a takarar tasa da Donald Trump.

Biden ya wallafa a shafin sa X cewa zai kasance a mukamin sa na shugaban kasar Amurka kuma shugaban rundunar sojojin kasar har zuwa lokacin da wa’adin mulkin sa zai kare a watan janairun 2025.

Haka kuma yace zai yiwa Al’ummar kasar jawabi a cikin wannan makon mai kamawa.

An dai ta kai ruwa rana kafin shugaban kasar kuma dan takarar shugabancin kasar a karkashin inuwar jam’iyyar Demukrat ya janye daga takarar bisa zargin tsufa da kuma rashin ingantacciyar lafiyar kwakwalwa.

”A lokacin da muka ɗauka muna mulki mun samar da muhimman abubuwa ciki har da dokar mallakr bindiga”.

Shugaban ya kuma goyi bayan mataimakiyar Kamala Haris a matsayin wadda za ta yi takarar shugabancin ƙasar a madadinsa.

”A yau ina son in jaddada cikakken goyon bayana ga Kamala a matsayin ‘yar takarar shugabancin ƙasar a ƙarƙashin inuwar jam’iyyarmu, lokaci ya yi da za mu haɗa kai wuri guda domin kayar da Donald Trump”, kamar ya wallafa a shafinsa na X.

A makon da ya gabata ne gwaji ya tabbatar da cewa shugaban ya kamu cutar korona, inda ya killace kansa a gidansa da ke Delaware, to sai dai a ranar Juma’a ya ce ya samu sauƙi, kuma zai ci gaba da yaƙin neman zaɓen sa cikin makon mai zuwa.

A baya dai shugaban ya ce ”Allah ne kawai” zai hana shi tsayawa takara bayan da aka yi matsa masa lamba kan ya haƙura da takarar, to sai dai daga baya ya ce zai iya haƙura da takarar bisa sharaɗin lafiya..

A baya-bayan nan dai shugaban ya fuskanci matsin lamba daga manyan ‘yan jam’iyyarsa da ke kiraye-kirayen ya haƙura da takara, tun bayan rashin katabus a muhawarsa da Donald Trump.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp