Home DUNIYA Biden ya janye daga takarar Shugabancin kasar Amurka

Biden ya janye daga takarar Shugabancin kasar Amurka

Shugaban kasar Amurka Joe biden ya dakatar da yakin neman zabensa a ranar lahadi.

wannan ya biyo bayan hukuncin da jam’iyyar sa ta demukrat ta yanke kan ingancin lafiyar kwakwalwarsa, da kuma binda take gani matsami nakasu a takarar tasa da Donald Trump.

Biden ya wallafa a shafin sa X cewa zai kasance a mukamin sa na shugaban kasar Amurka kuma shugaban rundunar sojojin kasar har zuwa lokacin da wa’adin mulkin sa zai kare a watan janairun 2025.

Haka kuma yace zai yiwa Al’ummar kasar jawabi a cikin wannan makon mai kamawa.

An dai ta kai ruwa rana kafin shugaban kasar kuma dan takarar shugabancin kasar a karkashin inuwar jam’iyyar Demukrat ya janye daga takarar bisa zargin tsufa da kuma rashin ingantacciyar lafiyar kwakwalwa.

”A lokacin da muka ɗauka muna mulki mun samar da muhimman abubuwa ciki har da dokar mallakr bindiga”.

Shugaban ya kuma goyi bayan mataimakiyar Kamala Haris a matsayin wadda za ta yi takarar shugabancin ƙasar a madadinsa.

”A yau ina son in jaddada cikakken goyon bayana ga Kamala a matsayin ‘yar takarar shugabancin ƙasar a ƙarƙashin inuwar jam’iyyarmu, lokaci ya yi da za mu haɗa kai wuri guda domin kayar da Donald Trump”, kamar ya wallafa a shafinsa na X.

A makon da ya gabata ne gwaji ya tabbatar da cewa shugaban ya kamu cutar korona, inda ya killace kansa a gidansa da ke Delaware, to sai dai a ranar Juma’a ya ce ya samu sauƙi, kuma zai ci gaba da yaƙin neman zaɓen sa cikin makon mai zuwa.

A baya dai shugaban ya ce ”Allah ne kawai” zai hana shi tsayawa takara bayan da aka yi matsa masa lamba kan ya haƙura da takarar, to sai dai daga baya ya ce zai iya haƙura da takarar bisa sharaɗin lafiya..

A baya-bayan nan dai shugaban ya fuskanci matsin lamba daga manyan ‘yan jam’iyyarsa da ke kiraye-kirayen ya haƙura da takara, tun bayan rashin katabus a muhawarsa da Donald Trump.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp