Home General Kungiyar Matasan Arewa ta Janye zanga-zangar data shirya a yankin

Kungiyar Matasan Arewa ta Janye zanga-zangar data shirya a yankin

Ƙungiyar Shugabannin Matasan Arewacin Najeriya ta janye zanga-zangar da ta shirya gudanarwa a faɗin ƙasar.
Shugaban Ƙungiyar shuwagabannin Matasan Najeriya Kwamared Murtala Mohammed Gamji ne ya sanar da hakan, ta cikin wani taron manema labarai da suka gudanar yau a Abuja, inda ya ce sun janye ƙudirin nasu ne a sakamakon yadda suka yi zargin sheɗanci ya shigo cikin shirin nasu.
Jaridar GTR ta ruwaito Gamji na cewa sun ɗauki matakin ne biyo bayan yadda suka gano wasu ɓata gari suna shirya wani mummunan abu, ta hanyar fakewa da zanga-zangar domin rikita ƙasar gaba-ɗaya.
A cewar Gamji ” Ni na fara shirya zanga-zangar kuma wasu mutane sun gayyace ni mun zauna dasu, harma suka shaida min so suke ayi zanga-zangar a iya Jihar Kaduna da Jos da kuma Babban birnin tarayya Abuja, saboda haka dole mu janye shirin namu tunda wasu sun fara yunƙurin cimma burinsu ta hanyar yin amfani damu”.
domin haka ya ce suna kira da dukkan wani ɓangare na al’ummar dake yankin arewa da suyi watsi dayin zanga-zangar, su dawo a haɗa kai abi hanyoyin da suka dace domin neman haƙƙin talakawan ƙasar a wurin shugabanni.
Bugu da ƙari ya kuma shawarci Jami’an tsaro da suyi gaggawar kama dukkan waɗanda suka fito zanga-zangar, domin tabbatar da tsaro da zaman lafiya a dukkan sassan Najeriya.
A ƙarshe ya jaddada cewa suna barranta kansu da yadda ake zagin Malamai, dama yunƙurin fakewa da zanga-zangar wajen lalata dukiyar mutane koma ƙona kayan Gwamnati wanda babu abinda zai haifar illa ƙarin wasu matsaloli a faɗin ƙasar.
PRNigeria hausa
 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp