Shugabar kungiyar mata ‘yan jarida ta kasa NAWOJ reshen jihar Kano, Hajiya Hafsat Sani da wasu jami’an kungiyar uku sun yi murabus daga mukamansu.
Sanarwar murabus din na zuwa ne yaiyn wani taron kungiyar da ya gudana a sakatariyar kungiyar Yan Jarida a ranar Litinin. Hafsat Sani tace sun yi murabus ne sakamakon wani dalili na kashin.
Read Also:
Lokacin da ta ke karin haske kan murabus, sakatariyar kungiyar Elizabeth Yila, ta bayyana cewa su ba zababbu ba ne a kungiyar rikon kwarya a ka ba su zuwa wani lokaci , Wanda su ka ga dacewar a yanzu su sauka su ba wa wasu dama.
Elizabeth ta kara da da cewa a Jagorancin da Suka yi sun gudanar da ayyukan da aka dora musu daidai gwargwado.
Baya ga shugabar kungiyar da sakatariya da Suka yi murabus akwai Kuma mataimakiyar sakatariya , Ruqayya Umar, da ma’ajin kungiyar Shamsiyya Ibrahim.
PRNigeria Hausa
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1190 days 9 hours 9 minutes 43 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1172 days 10 hours 51 minutes 8 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com