Kunyi zanga zangar 2012 amma kuma zaku hana matasa a yanzu – Atiku

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya soki Gwamnatin Tarayya kan ƙoƙarin dakatar da zanga-zangar da ake shirin gudanarwa a Nijeriya saboda matsin rayuwa a ranar 1 ga watan Agusta.

Atiku ya bayyana yunƙurin da abun dariya, saboda waɗanda ke ƙoƙarin hana zanga-zangar su ne waɗanda suka yi wa tsohon Shugaban Ƙasa Goodluck Jonathan zanga-zanga a shekarar 2012.

Zanga-zangar, wadda matasa suka shirya, na da nufin jawo hankali kan ƙaruwar yunwa da wahala da ’yan ƙasa ke fuskanta.

Masu shirya zanga-zangar sun ce za a shafe kwanaki 10 duba da halin matsi da ke ƙara ta’azzara, wanda suka ce akwai buƙatar kulawar gaggawa daga gwamnatin tarayya da na jihohi.

A wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook, Atiku ya jaddada cewa ‘yancin yin zanga-zanga yana cikin kundin tsarin mulkin Najeriya.

Ya buƙaci gwamnati da ta samar da yanayin tsaro da kwanciyar hankali don gudanar da zanga-zangar lumana, saboda ‘yan ƙasa suna da ’yancin gudanar da taro da bayyana ra’ayoyinsu.

Atiku ya soki gwamnati kan ƙoƙarin take waɗannan haƙƙoƙi, inda ya ce wannan ba ba ya cikin doka kuma yana barazana ga dimokuraɗiyya.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 16 minutes 43 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 10 hours 58 minutes 8 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com