Home General NLC ta musanta Janyewar shiga Zanga Zanga a Nijeriya

NLC ta musanta Janyewar shiga Zanga Zanga a Nijeriya

Ƙungiyar Ƙwadago ta Najeriya (NLC), ta ce bata janye daga shiga zanga-zangar matsin rayuwar da ake shirin gudanarwa a ƙasar ba.

Ƙungiyar ta sanar da hakan ne ta cikin wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na X, inda ta barranta kanta da labarin da ake yaɗawa na cewa ta fasa shiga zanga-zangar.
Sanarwar da Shugaban Ƙungiyar na ƙasa Kwamared Joe Ajaero ya sanyawa hannu ta ƙara da cewa, duk da ba ƙungiyar ce ta shirya zanga-zangar ba amma hakan bazai hana ta shiga ba, saboda halin ƙunci da matsin da talakawan ƙasar suke ciki a sakamakon wasu matakan da gwamnatin ƙasar ta ɗauka.
Adan haka ne ƙungiyar za ta shiga zanga-zangar domin taya al’ummar ƙasar wannan yaƙi, na nema wa kansu sauƙi a cikin mummunan halin da suke ciki.
Haka kuma ta buƙaci Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya zauna da masu shirya zanga-zangar a teburin sulhu, dangane da buƙatun da suke dashi ta yadda za’a magance matsalar ba tare amfani da ƙarfin mulki ba.
A ƙarshe ƙungiyar tayi fatan Gwamnatin tarayya dana jihohi zasu waiwayi koken ‘yan ƙasar, kuma su biya musu dukkan buƙatun su domin gudun faɗawar ƙasar cikin yanayi da ba’a tsammani.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp