Gwamnatin Kano ta saka dokar hana fita ta tsahon 24

Gwamnatin jihar kano ta saka dokar hana fita ta tsawon sa’oin 24, bayan bata – gari sun shiga cikin masu gudanar da zanga zangar lumana a jihar.

Gwamnan jihar Abba Kabir yusuf ne ya bayyana hakan yayin da yake ganaw da anema labarai a fadar gwamnatin jihar a yammacin Alhamis dake matsayin ranar farko ta fara zanga zangar.

Ya ce an saka dokar ne domin a dakile sace-sace da fashe-fashen kayan gwamnati da na al’umma da wasu ɓatagari ke yi a ƙarƙashin zanga-zangar.

Ya ce wasu ‘Yan siyasa ne da ba sa son ci gaban Kano ke daukar nauyin yan daba wadanda su ka fake da zanga-zanga su ka fara kai hare-hare.

Ya kuma umarci jami’an tsaro da su gaggauta fara aiwatar da dokar nan take.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com