Home Labarai Gwamnatin Kano ta saka dokar hana fita ta tsahon 24

Gwamnatin Kano ta saka dokar hana fita ta tsahon 24

Gwamnatin jihar kano ta saka dokar hana fita ta tsawon sa’oin 24, bayan bata – gari sun shiga cikin masu gudanar da zanga zangar lumana a jihar.

Gwamnan jihar Abba Kabir yusuf ne ya bayyana hakan yayin da yake ganaw da anema labarai a fadar gwamnatin jihar a yammacin Alhamis dake matsayin ranar farko ta fara zanga zangar.

Ya ce an saka dokar ne domin a dakile sace-sace da fashe-fashen kayan gwamnati da na al’umma da wasu ɓatagari ke yi a ƙarƙashin zanga-zangar.

Ya ce wasu ‘Yan siyasa ne da ba sa son ci gaban Kano ke daukar nauyin yan daba wadanda su ka fake da zanga-zanga su ka fara kai hare-hare.

Ya kuma umarci jami’an tsaro da su gaggauta fara aiwatar da dokar nan take.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp