Home Labarai Majalisar Addinai a Nijeriya ta bukaci a kawo karshen Zanga Zanga a...

Majalisar Addinai a Nijeriya ta bukaci a kawo karshen Zanga Zanga a kasar

Majalisar jagororin addinai ta Najeriya ƙarƙashin jagorancin Sarkin Musulmi kuma shugaban majalisar ƙoli ta harkokin addinin musulunci ta Najeriya (NSCIA), Alhaji Muhammad Sa’adu Abubakar III, da shugaban ƙungiyar kiristoci ta Najeriya (CAN) Archbishop Daniel Okoh sun yi kira da a gaggauta kawo ƙarshen zanga-zangar adawa da matsin rayuwa da ke gudana a faɗin Najeriya.
Sun yi wannan kiran ne a yau Juma’a cikin wata sanarwa da suka sanyawa hannu tare da babban sakataren majalisar NIREC, Farfesa Cornelius Afebu Omonokhua.
“Majalisar NIREC ta lura da abubuwan da ke faruwa a ƙasar a halin yanzu. Zanga-zangar wanda aka faro cikin lumana a ranar Alhamis, 1 ga watan Agusta, 2024 ta ɗauki wani salo na tashin hankali daga baya.
Sanarwar ta ƙara da cewa “A cikin ƴan sa’o’i kaɗan an yi asarar rayuka da dukiyoyi sakamakon wannan mummunan yanayi.”
Majalisar ta amince da cewa ana fuskantar wahalhalu da dama a ƙasar amma ta ce tashin hankali ba shi ne mafita ba, inda ta ƙara da cewa hakan zai ƙara dagula halin da al’ummar ƙasar ke ciki.
“NIREC tana kira ga ƴan Najeriya da su janye wannan zanga-zangar su baiwa gwamnati damar wanke kanta.” In ji sanarwar
A ƙarshe NIREC ta buƙaci gwamnati da ta gaggauta ɗaukar matakai domin biyan buƙatun ƴan ƙasar.
PRNigeria hausa
 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp