Home Labarai Sojojin Nijeriya zasu dauki mataki muddin aka cigaba da barna a zanga-zanga...

Sojojin Nijeriya zasu dauki mataki muddin aka cigaba da barna a zanga-zanga – CDS

Rundunar sojin Nijeriya tace zata saka hannun muddin tashe tashen hankula suka cigaba da aukuwa a wasu jihohin kasar nan sakamakon zanga – zangar yaki da talauci da tsadar rayuwa.

Shugaban dakarun soji Janar Christopphare Musa ne yabbayan hakan, yayin da yake ganawa da manema labarai a birnin tarayya Abuja, inda yace dakarun sojoji zasu fita domin magance wasu tashe tashen hankula ta baranatar da dukiya dake faru a wasu sassan kasar nan.

Rahotannin sun bayyana cewa sakamakon zangar zangar ya haifar da mutuwar akalla mutane 17 a birnin Abuja, kano niger, Borno, Kaduna da kuma Jihar jigawa, inda aka balle bankuna wuraren kasuwanci, yayin da hanyoyi da dama aka lalata su.

A wasu sassan kasar nan zanga-zangar ta cigaba bayan da aka yi arangama tsakanin dakarun ‘yan sanda da masu zanga-zangar a fadin kasar nan.

Christopher yace suna sane da yunkurin Al’umma na yin zanga-zanga domin nuna bacin ransu kan tsadar rayuwar da suke ciki a fadin Nijeriya.

Daga bisani ya bukaci Al’ummar Nijeriya dasu hada kai, wajen kawar da kai da kuma haramtawa kan su daukar kayan mutane a yayin da kuma bayan zanga-zangar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp