Home Labarai Tinubu yana kallon yadda ake gudanar da zanga-zanga a Nijeriya – Bagudu

Tinubu yana kallon yadda ake gudanar da zanga-zanga a Nijeriya – Bagudu

Shugaban kasa Bola Tinubu na kallon yadda zanga-zangar adawa da tsadar rayuwa ke gudana a fadin kasar nan.

Ministan Kasafin Kudi da Tsare Tattalin Arziki, Atiku Bagudu ne ya bayyana hakan yayin wata hira da aka yi da shi a gidan talabijin din channels.

Zanga-zangar da ake yi a kasar nan na da nasaba da tsadar rayuwa, da tabarbarewar farashin Naira da kuma cire tallafin man fetur da gwamnatin Tinubu ta yi.

Ko da yake an yi ta kiraye-kirayen ga Tinubu ya yi jawabi ga al’ummar kasar bayan zanga-zangar ta shiga kwana na uku, amma har yanzu shugaba Tinubu bai yi hakan ba.

Sai dai Bagudu, ya ce shugaban na Nijeriya ya san halin da ake ciki sosai.

Kamar yada suma ministoci ke da nauyi a kan su, ya zame musu wajibi subi yada zanga-zangar ke gudana.

Ministan wanda ya amince da cewa ana shan wahala a kasar nan, amma gwamnatin tarayya na kokarin ganin an samu saukin rayuwa ga ‘yan kasar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp