Home Labarai Nijeriya na kashe dala miliyan 600 a tallafin mai duk wata –...

Nijeriya na kashe dala miliyan 600 a tallafin mai duk wata – Wale

Ministan kudi da tattalin arziki na Najeriya Mista Wale Edun, ya ce kasar na kashe dimbin kudin da ya kai dala miliyan 600, kwakwankwacin sama da naira biliyan 956.370 a duk wata wajen siyo mai daga waje saboda makwabtan kasashe na cin moriyar man na Najeriya.

Mista Edun ya bayyana haka a wata hira da gidan talabijin na AIT, inda ya ce wannan shi ne ya sa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya janye tallafin mai, saboda Najeriya ba ta san ainahin adadin man da take amfani da shi ba a cikin gida.

Ministan ya ce kasashen da ke amfani da man da Najeriyar ke siyowa daga waje ba wai makwabtanta ba ne na kusa har ma zuwa Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya wato Santara Afirka.

Ya ce, ”ba Najeriya kadai muke sayo wa ba, muna saya wa kasashe ta gabas, har zuwa Afirka ta Tsakiya. Muna saya wa kasashe na arewa, muna saya wa kasashe na yamma.

Saboda haka dole ne mu tsaya mu tambayi kanmu, har zuwa yaushe za mu ci gaba da yin haka, to wannan shi ne muhimmin abu da ya shafi tattalin arzikinmu.”

Ministan ya ce wannan shi ya sa dole Najeriya ta dauki tsattsauran mtaki kan matsalar saboda tana hana bunkasar tattalin arzikin kasar.

Hukumar kididdiga ta kasar ta ce, yawan man da kasar ke shigowa da shi daga waje ya ragu zuwa kusan lita biliyan daya a wata bayan da Tinubu ya cire tallafin man, ranar 29 ga watan Mayu na bara.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp